*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*ALHMDLLH MUTANEN ƘARANGIYA BA ABUN DA ZAN CE DA KU SAI GODIYA, SABODA KUN NUNAWA LITTAFIN ƘAUNA FIYE DA YANDA NAYI TUNANI, TSAKANINA DA KU SAI SAMBARKA DA SON SO IRIN NA FISABILILLAH😍 ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MAKU HAR GADON BACCINKU*
*Lamba ta 52*
Ko kafin Safwan ɗin ya zo tuni Dije ta yi wankanta tsaf ta shirya, cikin zuciyarta cike take da ɗokin zuwan na shi saboda ta bashi haƙuri akan abunda ta yi masa, duk da kuma wani sashen na zuciyarta cike yake da jin nauyin haɗuwarta da Hajiya Mama, saboda yanda ta kamo hanya abinta ba tare da ta yi sallama da ita ba, bayan ta gama kammala duk abunda zata yi ne tace da Inna tana so ta je ta yi sallama da Inna Gambo, Inna tace ba inda zata je har sai Mijinta ya zo, ta ɓata fuska tace
"Inna fa sauri zan yi inje in dawo don kada ya zo yace sauri yake yi ba zai bari inje ba"
Inna tace "sai ki lallasheshi ai tunda kina son ya barkin"
Suna cikin wannan diramar ne suka jiyo ihun yara da saukar mota a ƙofar gidan, Dije ta diririce tace
"Kinji ko Inna gashi nan ma har ya zo ban tafi ba"
Inna ta maka mata wata uwar harara ta ce, "da kin je ai da zai ɗaukemu mutanen banza in ya zo bai taradda ke ba.."
Sallamar Usmanu da shi Safwan ɗin ne ya katse maganar Inna ta yi saurin faɗawa ɗaki ta sako hijabi ta fito suna gaisawa, Dije Usmanu yana baza masa tabarma da nufin ya zauna yace
"Ai da ka barta tafiya zamu yi saboda kada mu yi dare sosai kafin mu isa Gombe"
Usmanu ya kalli Inna yace "Ina Baffah su yi sallama to don naga baya gidan??"
Inna tace "yanzu nan zaka ganshi don bai daɗe da fita ba"
Usmanu ya baza tabarmar Safwan ya zauna yana kallon Dije dake zaune saman turmi tana yankan akaifa, don tun da ta gayar da shi ta sha jinin jikinta.
Baffah ya shigo cikin sauri yana yi wa Safwan Barka da zuwa bayan sun gaisa ne Baffah ya yafito Dijen ta taso jiki a sanyaye saboda yanda take jin gabanta yana faɗuwa tun lokacin da ta yi ido biyu da Safwan ɗin, saboda wani sihirtaccen kallon da ya jefeta da shi, ba shiri ta yi saurin kawar da idonta, shiyasa ko da ta zo wurin Baffan bata bari sun haɗa ido ba ta zauna gefen Baffan, Baffah ya kalli Safwan yace
"Bakina ba zai gaji ba wajen baka haƙuri akan ƙurciyar Dije, don ALLAH ka ƙara lurar da ita akan duk abunda ka ga ta yi na rashin kyautawa, kai kuma ka ji tsoron Allah ka riƙe matarka Amana, sannan ka yi mata uzuri akan abunda ta aikata a bisa kuskure"
Safwan ya sunkuyar da kanshi yace, "ba komi Baffah insha ALLAHu komi ya wuce kuma ma hakan bazata sake faruwa ba, adai ci gaba da yi muna addu'a kawai saboda addu'arku tana da tasiri sosai garemu"
Cike da jin daɗin zancenshi Baffah ya kalli Dijen yace "ke kuma ki yiwa Mijinki biyayya duk abunda ya ce dake ki yi kar kiyi masa musu ki amince, saboda in yasan abun nan ba mai kyau bane kema kinsan ba zai ce ki aikata ba, don haka yi nayi bari na bari shine halin matayen kirki, saboda haka kiyi ƙoƙari kiyi koyi da halin mahaifiyarki don kin fi kowa sanin yanda take zama dani, saboda haka kema ki koya ki zauna da Mijinki cikin girmamawa, ALLAH ya yi maku albarka ya baku zaman lafiya a cikin zaman aureku"
Daga Dijen har Inna har shi Safwan ɗin da Usmanu da ke tsaye sai "Ameen Ameen" suke faɗi, Inna tace ta je ta ɗauko Hijabinta sabo da ta bar mata, Safwan ya ciro kuɗi a masu dama ya ajiye gaban Baffah sannan ya miƙe, cike da jin daɗi Baffah yace

YOU ARE READING
DIJE ƘARANGIYA
Aktuelle LiteraturLabarine mai cike da barkwanci tare nishandarwa da fadakarwa a fakaice don kuwa zai saka mai karantashi ya ƙyaƙyata har ma ya faɗo kan gado ba tare da ya san yayi ba saboda dariya zai saka mutumcikin farin ciki marar misaltuwa.