*💣 DIJE K'ARANGIYA💣*
*NA HADIZA D/AUTA*
*TAURARI WRITER'S ASSOCIATION*
*Don Allah masu neman book ɗin Ƙarangiya daga farko ku yi haƙuri idan an kammala za ku sameshi a complete ɗinshi, plss ku yi haƙuri kunji😢saboda anyi nisa sosai kuma bana son kuna tambaya baku samu ba😆*
*Lamba 68*
Daren ranar Dije da Inna sai hira suke ta zubawa, don ita Hansai tun da ta ji cikinta ya ɗauka ta baje abunta sai sharar baccinta take yi ita da yaronta, ganin dare ya miƙa ne Inna ta ce da Dijen ta tashi ta je wurin Mijinta, Dije tana zumɓuro baki ta ce
"Anan zan kwana Inna mu yi ta firarmu Ni da ke Inna, sabida ALLAH yaushe rabon da mu ga juna an daɗe fa? Ni dai don girman ALLAH Inna ki barni in kwana abuna anan ɗakin"
Ta ƙare maganar tare da zubowar wasu ƙwallah, Inna ta gyara ta yi kwanciyarta tana faɗin
"To Ni dai bacci nike ji idan ke baki gaji da firar ba ki ci gaba ai akwai aljanun dare suna saurarenki zasu tayaki yin firar"
Dije ta zaro ido tuno abunda ya taɓa faruwa a school ta yi saurin kwanciya bayanta ta ƙudundune tana faɗin
"Inna ki yi man addu'a kar su kamani don ALLAH"
Inna ta miƙe zaune cike da mamaki ta ce "zaki ta shi ki je wurin Mijinki ko ko so kike yi ya ɗaukemu waɗanda basu san abunda suke yi ba?"
Dije ta miƙe tana kallon ƙofa tace
"To mu je ki rakani WALLAHI tsoro nike ji"
Inna ta riƙe baki cike da mamaki ta ce
"Tunda kike gidan baki ji tsoro ba sai yanzu da kika ga mun zo ko? To ya yi insha ALLAHu gobe tun da sassafe mu zamu bar maki gidanki tunda so kike yi ya ɗaukemu mutanen banza"
Dije ta miƙe ta fito Inna ta rufo ɗakin zuciyarta cike da nauyin kada Safwan ɗin ya ga sun riƙeta, aikuwa Dije cikin sanɗa ta ke tafiya tana waige sai jin ta yi anyi caraf da ita, ba shiri ta yage baki da nufin fasa ƙara taji bakin Malaminta cikin nata, gano shine yasa ta ƙara ruƙunƙumeshi jikinshi tana faɗin
"Mu je ɗaki tsoro nike ji"
Cike da jin daɗi ya sake manneta jikinshi suka yi ɗakinshi, ganin da gaske tsoron take ji yasa ya fara tambayarta abunda ya tsoratata, cikin murya ƙasa ƙasa ta yi masa bayanin yanda suka yi da Inna, cikin dariya ya ce
"ALLAH ya biya Inna da gidan Aljannah don Ni ta kyauta man, saboda tun ɗazu da na dawo wurinsu Baffah nike ta juye juye Ni kaɗai akan gado, dole na fito falo na zauna ina kallo nan ma na ji ba daɗi na kashe ina tunanin yanda zan yi in ce ki zo, ashe Inna tasan ƙishina shiyasa ta koro man ke waje"
Dije ta tureshi cikin fushi ta ce "tunda haɗe man kai kuke son yi ai ku je ni ma gobe wurin Hajiyarmu zan kwana "
Safwan ya janyota jikinshi ya ce "ai Hajiyarmu ma ba zata so ki bar Mijinki shi kaɗai ba yana kewa ba"
Haka ya hilaceta ya gwangwaje abunshi tare da sassafta murya wurin sambatun da ya saba, don gudun ya tafka abun kunya gaban surukai.
Tun da Sassafe aka kammala masu komi na breakfast ɗinsu tare da taimakon wasu yan aiki biyu da Hajiyar ta ƙaro masu, bayan sun karya ne aka sake wata sabuwar gaisawa sannan Safwan ya kwaahesu zuwa gidansu su gayar da Hajiyar, tarba ta mutumci Hajiya Mama ta yi masu fuska cike da fara'a tamkar cewa da man cen ƴan'uwanta ne, Inna da Baffah suka yi godiya sosai akan yanda take kulawa da Dije tamkar itace ɗiyarta ba Safwan ba, Inna da Hansai da Dijen sun daɗe gidan tare da Hajiya Mama sannan Safwan ya dawo da su Baffah da ya je kaisu yawon ganin gari, marece sakaliya ya ɗaukesu ya kaisu gidan Mijin Surayyy, inda itama ta yi masu tarba mai kyau tamkar kar su rabu saboda kirkin Surry ba ƙaramin burge su Inna yake yi ba, sai gaf da magriba suka dawo gidan inda suka taradda an haɗa masu abincin dare mai rai da lafiya, tuwon farar shinkafa da miyar agusi ta ji zuƙa zuƙan namomi tare da lafiyayye ferfesun kajin turawa masu manyan tsokoki, bayan sun ci abincin ne aka koma yin firar bankwana saboda tun da sassafe zasu juyawa inda suka fito, tun cikin daren Safwan ya tanadar masu duk abunda zai ba su ya basu, Hajiya Mama ma da nata kalar tsarabar Surayya ma da tata, haka suka yi ta godiya kamar ba gobe, don kuwa su kansu sun san ba ƙaramin arziƙi suka yi ba,saboda bancin sutura kuɗi tsabarsu dubu ɗari Safwan ya baiwa Baffah, Inna dubu Hamsin Usmanu da talatin Hansai ashirin yaronta goma, bayan suturar da aka cikasu da ita da turaruka da sabulai kala kala, yaron Hansai kanshi ledar kayanshi daban aka siyo mashi masu ɗan karen kyau.

YOU ARE READING
DIJE ƘARANGIYA
Fiksi UmumLabarine mai cike da barkwanci tare nishandarwa da fadakarwa a fakaice don kuwa zai saka mai karantashi ya ƙyaƙyata har ma ya faɗo kan gado ba tare da ya san yayi ba saboda dariya zai saka mutumcikin farin ciki marar misaltuwa.