*BAK'AR SHUKA...!*
NA
*HAUWA A USMAN*
~ JIDDARH~Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh
ArewaBooks:HauwaAUsmanjiddarh4️⃣0️⃣
Ihuuu ta soma yi da k'arfi tana wutsil-wutsil da k'afarta, amma ko'a jikinsu suka shigar da ita cikin kangon ya kwantar da ita saman buhu ya raba k'afa akanta ya soma k'ok'arin cire wondonshi, " hau ka sauka ka bani, Bahbah ya fad'a yana k'arasowa wajen, "mu kuma duk muna nan muna kallanku ko?
"Sai dai muyi mata rufdugu gaba d'ayanmu, d'aya cikinsu ya fad'a, zindir Gogo yayi had'i da rankwafuwa kanta yana niyyar saka mata jijiyarshi a jikinta, ihuuuun ta rink'a yi da k'arfi tana kai musu duka hannu bibbiyu, nan fa ta haukace musu da duka da ihuuu ta rink'a rarumar duwatse da k'asa tana watsa musu tana daga kwancen, " kai kutumar dumadu kaga yarinya da k'arfin hali, ke dan tsakiyar tsohonki ba taimaka miki zamuyi ba?
"Naga ai bamu kad'ai ne zamu ji dad'in ba har dake kaga shegiya, kai ku turmushe min ita, gaba d'ayansu sukayi kanta, wani ya rufe mata baki sauran suka rink'e k'afarta da hannayenta, duk da hakan bata bari ba ta cigaba da motsi da jikinta tana d'ago mazaunanta, ganin hakan ba kai mata zayyi ba yasa ta gantsarawa wanda ya rufe mata baki cizo da k'arfin tsiya, ya janye hannunshi da sauri tare dayin k'ara, cikin azaba ya shiga yarfa hannun, "bura uba cizo, batayi tsammani ba sai jin saukar marika tayi a fuskarta, kafin ta gama dawowa hayyacinta ya saka k'afa ya take mata ciki da k'arfi cikin mugunta harda cije leb'enshi.
Yadda kasan walk'iya haka k'afar tashi daya d'ora saman cikinta ta fita, daga shi da aka sarewa k'afar har sauran tsayawa sukayi suna kallan k'afar kafin daga baya ya saki mahaukacin ihuuun da duk ilahirin dajin sai da ya amsa, tsaye yayi kanshi duk'e rik'e da sharb'eb'iyar adda jini na d'aga, duk da a buge suke mankas sai da suka tsorata batare da sunyi magana ba suka juya zasu gudu, ya bisu da gudu, d'aya bayan d'aya sai da ya kashe su tasss suna ihuuun neman ceto amma a banza, sai da ya k'arar dasu tas, ya juya ya koma inda take kwance ta kasa tashi.
Da hannu d'aya ya d'agota ya sab'ata a bayanshi, a wahalce tace " ka sauke ni please bazan bika ba, wutsil-wutsil ta soma tayi tana san ta dare while tana ihuuu, ganin haka yasashi sanya hannu a gefen wuyanta ya d'ana d'as, cikin abinda baifi seconds biyu zuwa uku ba jikinta ya saki sakwaf alamar ta suma, ya bud'e bayan motarshi ya kwantar da ita kana ya cire mask d'in da daya rufe fuskarshi da bak'ar rigar jikinshi da safar hannun ya watsa su a bayan motar, ya bud'e butt d'in motar ya saka addar a ciki kana ya shiga yaja motar yabar wajen.
Bata farka ba sai da duhun dare yayi sosai da sauri ta mik'e ta ganta tsaye ita d'aya tal a tsakiyar daji ba gida gaba ba gida ba, cikin tashin hankali ta dafe kanta had'i da juyawa baya tana k'arewa inda take kallo, k'afa taja ta soma tafiya tana d'an gudu-gudu, sai da taci uwar tafiya takai ta kilo meter 30 kana ta isa makarantar da take kwana, cikin sand'a ta lallab'a ta shiga, alwala ta fara yi tayi sallah, yau ko addu'ar da take yi bata tsaya tayi ba bacci me nauyi yayi awon gaba da ita.
Sama-sama cikin baccin ta rink'a jin ihunn yara, a hankali ta bud'e idonta, yara d'alibai ta gani cunkus a kanta, da sauri ta mik'e tana bud'e idonta tar baya d'aliban suka soma ja cikin tsoro suna ihuuu, hakan ya jawo hankalin Malaman makarantar sukayo wajen, duk cikinsu babu wanda yayi gigin k'arasawa inda take dan a zatonsu mahaukaciya ce, d'aya daga cikin Malaman ya kwalawa me gadi kira da k'arfi, ya k'araso wajen da gudu hannunshi rik'e da zabgegiyar dorina, cikin fad'a da masifa Head Master makarantar yace " kana can kana sakarcin banza ka bar mahaukaciya ta shigo mana makaranta, k'asa yayi da kanshi cikin girmamawa yace " ayi hak'uri wallahi ban sani ba, "dama ta yaya za'ayi ka sani?
"Dalla fitar mana da ita, kafin ya k'arasa rufe bakinshi ya shinfid'awa Deeyanah dorina a gadon baya, zafin dukanne yasata firgicewa ta fita daga hayyacinta, k'ara zuba mata yayi da k'arfi, har sai da tayi ihuuu sosai, ta fita da gudu ya bita yana duka yara suka rufa musu baya suna ihuuu.
Suna b'acewa mutane ya bayyana a gaban me gadin, cikin matsanancin kuka soma girgiza kanta tana fad'in " a'a please! ka kyale shi, dan Allah karka yi mishi komai please dan...., bata k'arasa fad'ar abinda tayi niyya ba ya cakawa mutumin wuk'a a mak'ogwaro ya tsarga wuyanshi biyu, me gadin ya fad'i k'asa timmm, durk'ushewa tayi k'asa had'i da fasa rikitaccen kuka tana fad'in " na shiga uku, wayyo ni kaina wayyo ni Allah, kaico na, meye amfanin irin wannan rayuwar tawa?
"Meye amfanin haihuwa ta da iyaye na sukayi?
"Na zama bala'i a doron k'asa na zama silar mutuwar mutane bayin Allah da bazasu irgu ba, na zama masifa kuma annoba a cikin al umma, mik'ewa ta sake yi tsaye fuskarta cike taf da hawaye ta had'e hannayenta biyu waje d'aya tace " dan girman Allah, dan zatin Allah, dan darajar fiyayyan halitta ka kashe ni nima na huta please.
Sai da yayi gajeriyar dariya kana yace " in mutuwar kike so ke meyasa bazaki kashe kanki ba ko sai ni kike san na kashe ki?
"Ai kin fini sanin hanyoyin da zaki bi in mutuwar kike so da gaske, aina fad'a miki sai kin gwammaci mutuwa sau dubu Deeyanah, na fad'a miki saina lalata rayuwarki, zatayi magana ya d'aga mata hannu had'i da cewa " kije ki mutun mana waya hana ki?
Hawayenta ta goge da bayan hannunta ta soma tafiya tabarshi nan tsaye batare data sake cewa komai ba, gefen wani kango ta samu ta zauna a k'asa, saurin kallan kanta tayi cikin mamaki, bakinta bud'e tace " kodai bani bace an canja ni?
Ta fad'a tana bin kayan jikinta da kallo, an canja mata kayan jikinta ba wad'anda take sanye dasu bane, yanzu doguwar riga ce bak'a a jikinta an d'aura mata mayafin doguwar rigar a kanta, an yanke mata farcenta duka na k'afa dana hannu, saurin janye d'an kwallin kanta tayi ta shafa gashin kanta, shima an wanke mata shi tas an taje mata shi an gyara yaji man gashi, sai lokacin ta tuno jiya da zatayi alwala dataje tsarki taji wajen sub'ul wato har shaving aka yi mata, tashin hankali da rashin nutsuwar data ke ciki ne ya hana ta fahimtar komai har canjin kayan jikinta, wato jiya daya d'auketa abinda yayi mata kenan.
Dariya ta saka harda tafa hannu tana fad'in " habawa bani bace, dama nasan bani ce Deeyanah dana sani ba, tana dariyar ta fashe da kuka mai cin rai, ta dad'e nan zaune tana kukan kafin ta rarrashi kanta da kanta ta bawa kanta hak'uri ta goge hawayenta, ta d'an kishingid'a, rayuwarta ta baya ta shiga tunanowa da irin abubuwan da suka faru da ita.
Waiwaye.....
Siririn bak'in gilashin dake kan kyakkyawar fuskarshi ya cire, ya d'aga kanshi ya kalli sararin samaniya had'i da shak'ar iska da d'an k'arfi, a hankali cikin nutsuwa ya soma taka matattakalar jirgin yana sauka k'asa, cikin ranshi yana jin sanyin dad'i na ratsashi, daga wani b'angare na zuciyarshi tsoro na baibayeshi, bai san dalilin jin tsoron ba, amma yasan bazan wuce akan sab'anin da suka samu da Deeyanah ba daren jiya ba, yana fita daga harabar Airport d'in ya hangi su Azaan tsaye suna jiranshi, fuskarshi d'auke da bayyanan nan murmushi ya nufe su, caraf yaji an rik'e shi " Daddy sannu da zuwa, Deedee ya fad'a yana dariya, fad'ad'a fara'ar fuskarshi yayi ya sunkuya ya d'auke shi gami da jefa shi sama ya cab'e yana dariya.
"Nayi farin cikin ganinka My Son, Deedee yayiwa Deen kiss a kumatu yana dariya yace " meka kawo min Daddy?
"Da wuri haka?
"Aika bari na isa gida na huta ko?
Yayi mamakin rashin zuwan Deeyanah tararshi Airport har ya kasa hak'uri yace " Deeyanah bata zo bane?
"Inaga aiki take yi, danayi mata magana cewa tayi muje kawai, shiru kawai yayi bayyi magana ba dan bashi da abin cewa, Har suka isa gida Deedee yana rungume jikin Deen yana zuba mishi surutu wasu ya gane ya bashi amsa wasu kuma sai da ya bishi da un! u'u, yana d'auke dashi ya fito daga motar, ya nufi inda su Abbi da Babah suke tsaitsaye suna ta murmushi, cikin girmamawa ya durk'usa ya gaidasu suka amsa cike da fara, Abbi ya d'ora da " an dawo lafiya?
"Alhamdulillah yace yana dariya, cikin zolaya Babah yace " irin wannan dogon yaji haka?
"Bamu mukayi laifi ba amma harda mu a karb'ar hukunci, cike da jin kunya ya shafa kanshi, wajen su Ammu da Ammi ya shiga gaidasu, kana ya shiga part d'inshi, tasha kwalliya duk da bamai yawa bace, simple make up tayi, jikinta sanye da doguwar rigar bubu ta leshi, ta kashe d'aurin d'an kwalli.....
JIDDARH....

YOU ARE READING
BAK'AR SHUKA...!
SpiritualGurbatacciyar zuciya me cike da zallar soyayya, soyayyar da bata da alkiba, bata da gaba balle baya, soyayyar da tunda aka fara ta babu farin ciki da jin dad'i har izuwa k'arshenta, duk da sun kasance ma'aurata amma rayuwa suke gudanarwa a juye ta b...