84

2 1 0
                                    

*🎀🎀 SARFRAZ 🎀🎀*

*84*

*Na Hafsat Aliyu Shu'aibu Chikaji*

    Zare Ido yayi ya tsaya yana kallon Nawaz da mamakin ganinta tana Sallah, "dear jinin ya tsaya ne?" Sai kuma yayi shiru sanin babu me bashi amsa tunda Sallah takeyi

    Gefe yaja ya ɗauki medium ɗin luggage ya fara zuba musu kayansu, yawancin na Nawaz duka Abaya ya zaɓar mata, shima dai ba wasu kaya bane na Azo a gani ba.

    Yana gama shiryawa itama dai-dai lokacin ta idar da Sallar "my soulmate Naga kana haɗa kaya a akwati?"

    "Dear wallahi zuwa Abuja ne ya kama mu urgently, yanzu mum ta gama waya da Naufal wai mum ɗinsu ta rasu?"

    Duhu Nawaz ta shiga domin bata gane inda zancenshi ya dosa ba "dear waye Naufal?"

    "Au na manta baki sansu ba, yaran colonel ne Naufal da Fudail, Amma dama ba wannan data rasun bace ta haifesu, tun suna jinjiraye maman su ta rasu bayan ta haifesu, to shine a garin su aka  bashi auren wannan data rasun,  Matace mai karamci da mutunci sosai, munsha zuwa gurinta muyi hutu sanda daddyn mu yake raye, ƙawar mummy ce sosai."

    Rausayar dakai Nawaz tayi, irin Alamun tausayin nan, "Allah sarki, Allah ya jiƙanta yayi mata rahma yasa ta huta, mu kuma Allah ya bamu ikon yin Abinda mukazo duniyar yi"

   "Ameen dear thanks, yanzu muje muyi wanka saimu shirya saboda su mummy na jiranmu,"
    Tsayawa yayi yana kallonta sai kuma ya kanne ido ɗaya as usual "ko na tsaya na Angonce tukuna? Kinga sai muyi wankan mu me hujja koh"

    Ita dai Nawaz shiru tayi kanta a ƙasa batace komai ba, shima be kuma cewa komai ɗinba ya sunkuceta zuwa bathroom, "wasa nakeyi miki fa, ai yaci na barki kiɗan huta koda na kwana uku ne, kada naje a kuma yin tuntuɓe da wani cikin a bakin ƙofa"

    Duk da cewa Nawaz ba wani kunyarshi takeji yanzu ba amma Saida maganar shi tasata rufe ido tana dariya ƙasa-ƙasa.

    
   Bayan wasu Yan mintoci har sun shirya abinsu, tsaff sukayi gwanin ban sha'awa, sai tsokanar Nawaz Aayaan yake tayi barin ya lura tanata ɗan kannewa "yasan tsoron haɗuwarsu takeyi domin yasan da tasan zai shigo ya ganta tana Sallah da batayi lokacin ba.

      Ta ɓangaren Nawaz kuma duk sai take Dan jin fargaba na kamata kaɗan saboda yadda taga yanata nan-nan da ita, gashi dama an daɗe ba'a haɗu ba, kuma tasan Aayaan har dai ya chafke ka saiya ƙureka duka sannan zaice zai fara komai.
    Tunawa tayi da second night ɗinsu yadda tasha fama, Saida tsigar jikinta ta tashi saboda tunawa da tayi da irin aika-aikar da yayi mata, har kuka tayi wiwi akan ya dena amma ko'a jikinshi (wai an yakushi kakkausa).
    Ita ba komai ke damunta ba irin yadda yake tasa ta da taɓe-taɓe, taɓa chan taɓa nan, matsa nan, matsa chan, tsotsi nan tsotsi can, duk saiya ƙureta tass taji kamar numfashinta zai ɗauke, dama ace idan yazo Abinda yazo yi zaiyi ya wuce amma ita tasan ta shiga ukunta, duk abinda yasa jikinta yin sanyi kenan, barin dataga duk motsi saiya kashe mata ido tare da ɗaga gira.

     A falour suka haɗu dasu mum duka don tafiya Airport, mummy na matukar jin daɗin Yadda Aayaan da Nawaz suka fahimci junansu, Aseey ma haka.

  *Some hours later....*

 
     Su mummyn Aayaan ne da Aayaan ɗin da Aseey da Nawaz sai Muhsin, zaune a Babban falourn baƙi na gidan colonel, falourn cike yake da masu Amsar gaisuwa, kowa kagani kasan ba'a cikin kwanciyar hankali yakeba.
    Mummy ma sosai hankalinta ya tashi ganin da idan suka zo gidan ita marigayiyar suke gani taita hidima dasu.

     "Lokacin sallar magrib yayi, bari muje masallaci" cewar colonel yana miƙewa tare da dafa kafaɗar Aayaan, ita dai mummy na zaune sanye da hijabi tanata jan chasbaha.

SARFRAZ Where stories live. Discover now