Chapter 1 page 76

197 15 3
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 7⃣6⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*

Washe gari da safe kan su tashi an jere musu kayan break. Sai karfe goma suka tashi tare sukai wanka makale da juna. Shi ya shirya ta suka fito sai da suka karya. Falo suka dawo suka zauna. Ta kalli Muhammad tace
"Kai na yana duhu har yanzu!"

Ya kamo hannun ta yace
"Na sani Baby."
Sai yai shiru can yace
"Da farko dai ina mai baki hakuri da rashin fada miki asalin wanene ni!
Na duba na hanga na hango a rayuwar nan ba a fiya so dan Allah ba sai in kana da wani abu ko kudi,  kyau,  mulki da sauran su.
Tin ina makaranta na gane haka domin kyau na yasa da yawa yan mata ke so na. lokacin da aka san wanene ni baki ga yadda yan mata ke hauka akai na ba. Ni kuma sam Allah bai dauran son su ba ko kadan mace ma bata damen ba kallo bata ishen ba.
A haka na gama karatu na wanda a lokacin da su Ummi suka farai min zancen aure sai ya kasance zaba min suke saidai kawai suce naje naga yar wane? Ko yar wancan? Duk yayan masu kudi ne ko mukani. Wanda da naje kan na yaba sunin waye ni suke aminta ni kuma abinda bana so kenan na fiso a soni a yadda nake ba a matsayi na na dan wani ba."

Yai kissing hannun ta yace
"Na farai miki bayani ban fada muku asalin wanene ni ba ko?
To ni Muhammad ni kadai ne da namiji a wajen Abbi wanda Abbi shine sarkin wannan garin namu ana min lakabi da Yarima mai jiran gado. Tin asali ina da sanyin hali abin duniya bai damen ba wanda hakan yasa bana daukar kaina a matsayin wani. Wannan ya kara sa mahaifina ke sona da alfahari dani.
A makaratun ya'yan talaka nai karatu har na gama na fara jami'a ban fita waje ba a kasa ta nayi cikin garin mu. Bani da abokai dan ban fiya son ba saboda da yawa ba sa zama dan Allah da mutum kana zaune dasu ne suna cin dundunuyar ka. Aboki na basu wuce daya zuwa biyu ba suma ya'yan yan uwa ne sune kadai zance miki abokai na."

Ya dago ya kalle ta yace
"To ni a lokacin da naga haka shine na nemi Ummi nai mata bayani ta gane wacce irin mace nake so. Dan bana son a soni dan ni waye ko dan mahaifi na wannan shine yasa na taho garin ku.
Watana uku a garin ku ina bulayin neman matar da zan aura dan Ummi ta bani shekara tace in ban fitar ba kowa ta samu zara aura min.
A wata ukun nan na hadu da yan mata wanda wasu in na tsayar wulakanci suke min sun rainani da sauran su.
Wata rana ina zaune akan layin ku naga fitowar ki da hijab har kasa daga kallo daya zuciya ta, ta kamu da son ki tin daga ranar na fara bibiyar rayuwar ki na samu tarihin gidan ku da abinda ba zaki zata zan sani ba domin har Kamal sai da na shigewa na san halakar ku dashi.
Wanda farkon fara magana ta dake lokacin kika fito duk da baki tsaya munyi magana ba amman fuskar da kika bani kadai ya kwantar min da hankali. Wanda daga lokacin ban kara saki a ido ba har na lokaci mai tsa6i kuma hakan bai hanani nemanki ba har kika dawo nazo wajen ki da soyayya ta.........."

Ya numfasa yace
"Kinji komai duk halin da ake ciki Ummi ta sani amman ban fada mata halaiyar da na sameki a ciki ba."

Ta sauke ajiyar zuciya ta shige jikin sa tace
"Tayaya akai Baba ya yadda da maganar auren mu."
"Kamar yadda na fada miki na bibiyi rayuwar ki sosai anan na gane matsalar Baba ba auren ne baya so yayi muku ba kudin da zai kashe ne wannan yasa da naje neman auren ki na nuna bana bukatar komai wannan yasa ya yadda ya aminta."

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now