Chapter 1 page 78

185 14 1
                                    

*WANNAN RAYUWAR💐💐💐*
Based on true life story

Chapter One
page 7⃣8⃣

By
*MARYAM SULEIMAN INDABAWA (Antyy)*

*FATIMA MUHAMMAD SANI (ZarahArkel)*
*HALIMA MUHAMMAD SUNUSI (Barrister S@dy)*

🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
*Hakuri da Juriya Online writer's (HAJOW)*✍🏻✍🏻✍🏻
🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐
(United we stand, our aim is to educate, entertain and enlighten our readers in a adventurous manner.)

Dedicated to *Hakuri da Juriya Online writer's Fans* (Allah bar zumunci da kauna)
Wannan littafin sadaukarwa ne ga daukacin masoyan Association din mu wato *HAJOW*



Zaune yake yayi nisa a cikin tunanin sa abubuwa sun masa yawa ya rasa yaya zaiyi ya zaiyi da Halima kuma ya zaiyi da Sadiya?

Hakika zai auri Halima ko dan taimaka mata ya fitar da ita daga halin da take dan yana tausaya mata yasan a irin wannan lokacin tana iya yin koma. Bama yai duba da karancin shekarun ta to yanzu yaya zaiyi tayaya mahaifin ta zai barta tayi aure a yanzu.

Wayar sa ya zaro ya fara neman layin Hajara. Tana dauka yace
"Hajara number wayar Yaya Hafsa nake so."
"Ok bari na turo."

"Aha ina Halima?"
"Tana daki!"

"Duba kiga me take?"
Mikewa tayi ta shiga ta same ta tana kwance tace
"Tana kwance."

"Bata wayar!"
Mika mata tayi tace
"Yaya kabir ne."

Amsa tayi tare da mikewa zaune sallama yayi wanda yasa gaban ta ya fadi. Da kyar ta daure ta amsa. Yace
"Me yake damun ki?"

"Ba komai!"
"A'ah ga muryar ki nan ta nuna damuwa a ciki. Bana hanaki saka damuwa da tunani ba."

"Tayaya zan daina damuwa da tunani Kabir?"
"Ta godiya ga Allah da dogaro dashi sai kiga ya kawo miki mafita nan take."

"Allah ya kawo min to."
"Yauwah koke fa! Kika sani ko Isma'il ya dawo yace yana son kk."

"Haba Kabir yanzu kai in yazo yace yana so na sai ka yadda!"
"To menene a ciki."

"Baka ganin abinda yai min. Bama wannan ba kana zaton Isma'il xai ga kimata in munyi auren ne nasan ba zai taba ba. Na riga na rasa kimar da ko wanne namiji ya auren zai gani a tare dani yaya zanyi ka fada min tayaya zan gyara wannan barakar."
"Ta komawa ga Allah sannan ki daina cire tsammani."

"Banda aiki sai neman gafar Allah."
"Haka nake so ina neman wata alfarma."

"Ina jin ki!"
"Dan Aah kada ki kara kuka."

Shiru tayi yace
"Kinji?"
"Naji!"

"Yauwah Allah miki albarka. Kinci abinci?"
"A'ah!"

"Why?"
"Na kasa ci."

"Ko a kawo miki wani abu ne?"
"A'ah zanci."

"Yauwah kici kinji."
"Nagode Kabir."

"No no kada kiyi wata godiya. Sai jima."
Ya kashe wayar. Ido ya lumshe yana mai sakin ajiyar zuciya.  Karar sako ne ya shigo wannan yasa ya bude ido. Number Hafsa ce.

Dauka yayi ya kira tana dauka suka gaisa yace
"Kabir ne!"

"Wanne?"
"Abokin saurayin Halima."

"Au Kabir ya kake ya gida?"
"Lafiya lou. Yaya Hafsa daman ina son na ganki ne?"

"To yaushe kenan?"
"Ko zuwa gobe ne."

"To Allah kaimh."
sukai sallama ya ajiye wayar take yaji wata matsalar ta kau. Sadiya ce ts fado masa wacce tin jiya da ta kashe waya take yaji wani iri nan da nan ya fara neman layin ta.

WANNAN RAYUWARWhere stories live. Discover now