Kainuwa.....12

6.6K 494 20
                                    

.. 🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*12*

Ana Magrib Magajiya ta kintsa tsaf sannan ta aikama da Sarki zuwanta, alokacin hankalin Mai Martaba ya gama tashi dan yana tasowa daga fada ya aika wani bafaden sa akan ya dubo masa lafiyar matarsa da d'ansa kafin yazo sai dai abin mamaki dawowa akai aka sanar dashi rashin isowarsu gidan.

Magajiya ta iso a lokacin shi kansa ya matso ya ganta dan yana san jin abinda ke faruwa.

Bayan ta shigo ne ta zauna a inda ta saba zama wato d'an nesa dashi kadan, sannan ta numfasa cikin isa da kuma nuna alamar damuwa tace " Ranka ya dade muna cikin matsala fa?"

Kallanta yai cikin mamaki sai dai bai amsa ba, itama ta kalleshi sannan tace " Basira bata dawo ba."

Kallanta ya sakeyi nan ma bai tanka ba, idanu ta runtse cikin alamar kunar zuci na tausayi tace " gobara ce ta kama da gidansu a daren jiya."

Lalai wannan kalma ta d'agamai hankali wanda bai san sanda ya mike tsaye ba, Magajiya ta kalleshi cikin kulawa tace " Yayanta da matarsa sun rigamu gidan gaskiya."

Sarki a tsaye yake kawai dan hankalinsa ya kai koluluwar tashi, ta cigaba tare da share idanu kamar irin mai kwallar nan, tace Basira da d'anta dai ba abinda ya samesu sai dai firgita datai da abin yasa ta fita da gudu wanda har safiyar yau ba wanda ya ganta.

Hankalin Sarki ya kara tashi ya koma Ya zauna dabas kamar ba sarki ba.

A hankali ta taso tazo inda yake tasa hannu ta kamo nasa hannun tace " nasani sarai hankalinka ya tashi sosai kamar yanda nawa ya tashi, shiyasa na rasa mai zance maka, Hisham tun safe yake nemanta amma ba labari wanda hakan ne yaga dole yazo ya sanar dakai asan abinyi."

Kallanta yai ji yake kamar ya saki wani irin ihu na bakin ciki, Magajiya cikin murya taban tausayi tace " Basira ba yarinya bace na tabbata zata dawo hankalinta ne ya tashi har yasa tai wani hannu sai dai fatan Allah yasa ta fad'a hannu na gari."

Sarki ya d'ago cikin tashin hankali wanda tunda Magajiya take bata taba ganinsa cikin wannan yanayin ba, kallanta yai cikin kakkausar murya yace " inasan kad'ai cewa."

Kai ta jinjina alamar to, sannan ta mike ba tare da tace komai ba tai waje.

Tana fita ta kalli kofar d'akin tai wani murmushi tace " kai da Basira sai a lahira dan duk yanda kaso ko ita taso baku isa ku kara zama tare ba bare har kaga d'anka ka fahimci menene d'a na jini."

Juyawa tai tacigaba da tafiya ana take mata baya cikin kasaita da tak'ama.

************

Shikam tana fita ya runtse idanunsa kam jiyai hawaye ya gangaro mai sau d'aya, mikewa yai yaje jikin tagar d'akin ya bud'e ya kurama taurari ido,jiyake kamar zuciyarsa zata fashe ga zuciyarsa ta fara masa sake sake mara amfani, yana tsaye yana kallan taurari sai dai a zahiri tunani ne fal ransa, nan ya shiga tunanin rayuwarsu da abokinsa da kuma matarsa ga kuma bai taba ma ganin d'ansa ba,kasa jure abinda ke ransa yai ya tsugunna a gun tare da dafe kansa wanda ya fara sara mai....

A wannan ranar Mai Martaba ko gadonsa bai hau ba bare ya samu danar rintsawa.

************

Basira ma bataga bacci ba a wannan ranar, tunani ne kawai ke mata yawo a ranta, ido ta kurama d'anta tana ji wani abu na taso mata, ya zatayi? Zama zatai tayi anan saboda tsoron kar wani abu ya samu d'anta? In tai hakan kenan ta raba d'anta da mahaifinsa, sannan auranta fa?"
Wad'annan tunanukan sun mata yawa fal aranta wanda sukasa idanunta suka kafe kaf.

KAINUWA....Where stories live. Discover now