Kainuwa....34

6K 481 32
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*34*

Washegari.

Da safe zaune yake a gaban Mai Martaba a cikin Turakarsa.
Mahaifinsa ya kalleshi cikin kulawa yace "Turab me yasa ka dawo tun jiya? Sannan tundaka dawo baka zo ba."

Fuskarsa a d'aure take dan sam ba fara'a a cikinta kallansa yai yace " Dama zuwa nai na sanar dakai zan auri Bilkisu yar gidan Sarkin kano."

" Alhamdulilah nagode kwarai na kuma ji dadi daka fahimceni."

"Bayan umarnin auranta daka bani a yanzu auranta yana tattare da amintata, a da auranta zanyi saboda umarninka, sai dai yanzu zan aureta ne dan kaina."

Fuskar mai martaba ta kara fadada da farinciki yace "naji dadi yanda kuka fahimci juna."
Kallan Mahaifinsa yai yanajin wani radadin takaici a ransa, yace " zan koma."
"Abu Turab!"
Komawa yai ya zauna sannan ya kalli Mahaifinsa dan yanda yaji ya kira sunansa yasan yana bukatar nutsuwarsa.

Mai Martaba ka kalleshi cikin kulawa yace " Abu Turab me yasa kake so ka b'oyemin abinda ke ranka? Me yasa bakasan mudinga raba damuwar dake zuciyoyinmu?"

Shiru yai sai dai zuciyarsa tadan raunana.
Sarki yace " Meke damunka?"
Shiru ya kuma yi sai dai a wannan karan ya d'ago ya kalli mahaifinsa da idanunsa da suka canza launi.
Sarki ya cigaba" Shikenan mubar maganar inhar zuciyarka bata san inji."
Abu Turab yace " zan koma Abba."
Mai Martaba ya murmusa yace " to Turab."
Mikewa yai ya fito daga bangaren mahaifinsa, ba shakka yanasan ya sanar dashi damuwarsa da kuma neman shawararsa sai dai ba yanda zaiyi domin kafin ya kasance mahaifinsa sarki ne shi a wannan garin dole kuma yai abinda ya dace a matsayinsa na sarkin garin.

Bangarensa ya nufa rike da sandarsa yana gana Garzali da wani na gefensa.
Sunsha kwanar da zata kaisu bangarensa yaji muryar Khadija tace " Ya Turab."
Haka kawai ta samu kansa da kin tsayawa dan abinda Mahaifinta sukamai bayaji ko ganin Khadija yana kaunar yi a wannan lokacin.
Ganin bai tsaya ba yasa ta kara sauri, har tazo inda suke, tace "Ya Turab."
Tsayawa yai sai dai bai juyo ba.
Gabansa ta dawo ta kalli Garzali tace " dan Allah kudan matsa kadan zanma Ya Turab magana."
Nan suka gaisheta suka matsa.
Kallansa tai tace " Yaya."
Bai kalleta ba sai dai yace " ya akai?"
Tace " yaya kana ganina?"
"Me kike nufi da hakan?"
Ta kara matsows tace " Yaya ninasan baka ganina, sai dai na rasa dalilin Abba na na zuwa ya fadama Magajiya wai kana gani."

Kallanta yai, ta kalleshi hakan yasa ya kauda idanunsa, tace " Yaya Please ka kula da su wlh sam hankalina ya kasa kwanciya dasu, na tabbata da abinda suke shiryama."

Jitai yace " yanzu kinaso ki cemin zuwa kikai kiban shawara akan kula da Mahaifinki? Ko kuwa zuwa kikai ki sanar dani Mahaifinki zai cutar dani?"
Cikin rashin fahimtar kalamansa tace " Ban fahimceka ba..
.."
" in mahaifinki zai cutar dani tayaya nake da tabbas din ke bazaki cutar dani ba?"

Kallansa tai a zabure cikin tsananin mamaki tace " Yaya."
Yace " da mahaifinki da ni wanene mafi kusanci dake? Wanene wanda yake jininki? Tayaya zan yarda zaki juya ma mahaifinki baya akan wani makaho wanda bakuda hadi dashi?"

Gaba daya ta ma kasa magana dan batada amsar da zata bashi, tana neman amsar da zata bashi taga ya fara tafiya.
Idanunta ne suka ciciko a hankali wasu zafaffan hawaye suka xubo mata, me yaya yake nufi?
Gani tai ya tsaya a jikin kofar bangaren Mahaifiyarsa da alama magana yake da wani, gani tai ya saki fuska ba kamar yanda ya cukule mata ba.

A hankali ta tako har gefen da suke.
Mairo ta gani a tsaye a gun rike da kula suna magana, juyawa tai zuciyarta sam ba dadi.

A bangaren sa kuwa, bayan ya taho daga gun Khadija zai wuce yaji tace " Ya Ina Kwana?"
Juyowa yai ya kalleta yace " Mairo kece?"
Tace " nice, Umma ce ta sani in kawo mata abu yau da safe."
Murmushi yai yace " Mairo kinaji da Umman nan."
Ta kalleshi tace " Da cemaka akai Ummanka ce kai kadai?"
Kallanta yai yace " Yar gidan Umma ce ke dama ai."
Zatai magana yace " ki gaisheta."
Tace " bazaka shiga ba?"
Kallanta yai fuska a sake yace " Later."
Daga nan yai gaba.
Kallansa tai cikin mamaki dan taga ba haka suka saba ba.

************

Abdulmajid ne zaune gun Magajiya yace " Umma ya kukai Jiyan? An bincika yana ganin?"

Magajiya ta kalleshi tace " Abdulmajid, ka nutsu sosai kaji abinda zan fada ma."
Kallanta yai sannan yace " inaji."

" Ka shiga hankalin sosai da Abu Turab ka daina masa kallan wanda bashida wayau ko bai san komai ba, wlh wnnan yaran hmmmm"
Tai shiru sannan tacigaba " kadai bi a hankali karka kuskura ka fada tarkwansa."

Abdulmajid ya dan tabe baki yace " ni Umma har wannan yaran ya kai in shiga hankalina a kansa?"
Ta kalleshi cikin isarta sannan ta ce " Abdulmajid kenan."
Kara tabe baki yai yace " ni Umma dama maganar aurena nazo muyi, nace tunda dai Bilkisu an riga an hadata da Turab mai zai hana mu juya akalar auran kan Mairo."
Ya karasa maganar yana dan sosai keya.

Kallansa tai tace " Mairo? Wacece hakan?"
Yadanyi kasa dakai yace " Mairo 'yar gidan Barde."
Barde?bakada hankali ne?"

Yace " Umma to...."
Katseshi tai cikin fada tace " nimeyasa baka tunani ne a al'amuranka? Abu Turab zai auri Gimbiya Bilkisu kai kuma dan hauka kacemin wata Mairo? Me yasa ne bazaka dinga abu da tunani ba?"

Fuska ya hade dan maganar ta batamai rai, Magajiya ta cigaba " kada ka kuskura ka karamin wannan banzan zancen."
Tana kaiwa nan ta maike tai ciki.
Kallo ya bita dashi da alama zai je gun Sarki ya fadamai kuwa dan shi kam Mairo yakesan aura ko ta wani haline kuwa, dan kwanan nan har mafarkinta yake wai sunyi aure.

🤣

**************

Kwana biyar da dawowarsu kuwa Mai Martaba Sarki Shu'aib mahaifin Bilkisu ya aiko mutane daga Masarauta akan amincewa da aure da sukai.

Wannan labari ya tadama Khadija hankali, sai dai duk yanda taso ganin Abu Turab abin ya faskara, itadai ba dama ta shiga bangarensa dan ya bada umarnin hana kowa shiga bayan Mahaifiyarsa, sannan ko a waje tadaina ganinsa.

Mairo ma wannan labarin ya d'aga mata hankali, sai dai ba yanda zatai dan dama ta riga tasan komai.

Yau ta gama aikin gida kenan tana 'yan kukuninta na takaicin abinda ake sata yi, wani yaro ne yazo ya sanar da ita ana san ganinta a waje.
Hijab dinta ta ja ta saka dan bata kawo saurayi bane ko wani na kunya ba.
Mamaki ya kamata kwarai ganin Abdulmajid a tsaye a jikin soron gidansu.
Kallansa tai cikin mamaki sannan ta karasa gunsa tace " Malam lafiya?"
Abdulmajid ya kallesta kalleta yace" Mairo ina kika shiga ne? Sam na daina ganinki dole kika sani na zaro jiki na fito."
Kallan sa tai tace " ban fahimci inda ka dosa ba."
Yace " Kin manta me nacemiki ne? Na dauka na sanar dake kedin matata ce."
Dariya ta saki tace " Matarka? A yaushe kenan akai hakan? A iya tunanina ban amshi sadakin ka ba."

Idanu yadan rage yace " An kusa ai indai wannan ne, inkuma kinaso in baki yanzu to."
Ka bani yanzu? Da alama tunanin ka ya fara tafiya ko?

Matsowa yai a zuciye hakan yasa ta matsa da sauri sannan ta nunashi da hannu tace " Stop Malam! Tsaya anan karka kuskura ka tabani."

Kallanta yai rai a bace yace " Mairo."
Tace " kwarai kuwa sunana Maryam wacce ake cewa Mairo yar gidan Barde kanada magana ne?"
Kwafa yai sannan yai murmushin mugunta yace " ina tausaya miki yarinya randa kika zo hannu."

Baki ta murguda tace kafa zanzo ba hannu ba.
Ta juya tai ciki ranta a bace.

Murmushi ya sakeyi sannan ya juya.

*TEAM ABU TURAB*

KAINUWA....Where stories live. Discover now