Kainuwa.....61

6.5K 529 65
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*61*

Jin bataji saukan mari ba yasa ta bud'e ido a hankali, kallansa tai sannan tai saurin zubewa a kasa ta saki wani irin kuka.

Turab idanunsa ne suka canza, kallo d'aya zakamai ka tabbatar da tsantsar b'acin rai, maganin nan ya cilla mata.
A tsorace ta d'ago jiginta ya hau karkarwa.
Cikin kakkausar murya yace " Waye ya saki?" ba wai dan baisan amsar bane, a'a yanaso yasan ko tana danasanin abinda takeyi.

Kasa ta karayi tana kuka sosai tace " Ranka ya dade ka yafe min wlh in na fad'a kasheni za'ai, sannan mahaifina karshensa yazo."

Magajiya? D'agowa tai da sauri jin abinda yace, yanayin kallan da tai yasan dama abinda yake zargi haka ne, kusa da kafaffunsa ta matso tace " Ranka ya dade wlh nima ba'a san raina nakeyi ba, mahaifina na bukatar aiki na gaggawa a asibiti shine akace in ina sa maganin nan za'a biyamai kud'in aiki, sannan komai ua faru in sanar da ita.

Fuskarsa ya shafa da hannayensa biyu a ransa yace Inalilahi wa ina ilaihi raji'un.
Zama yai a kan kujera sannan yace " me ya faru tsakanin Hajiya da Magajiya?gaskiya nakeso ki fadamin, ni zan taimakeki, zan kuma bayar da kudin aikin."

Tana kuka ta girgiza kai tace " wlh ban sani ba, nadai san a ranar da Umma Rabi tazo a ranar ta aika a kira Magajiya, sannan daga ranar aka fara sani aikin."

Turab ya kalleta yace " naji, zan sa Lantana ta koma dake bangaren Hajiya da kula da ita, zan gani ko kinyi dana sanin abinda kika aikata, sannan ki jira hukuncin da zansa a yanke miki, mahaifinki ni zan taimaka mai sai dai ke dole ki fuskanci hukunci."

Kuka take sosai tace " na sani Ranka ya dade, na gode kwarai da cetoni da kai daga cikin masifa."

Turab yace ta tashi ta tafi.
Fitowa yai, ya nufi can cikin gida bangaren kannen mahaifinsa dan zuwa gun Umma Rabi.

Ko Garzali baya yarda ya biyoshi duk da kuwa ya yarda da shi.
*********

Khadija kuwa ganin Turab ya shiga bangaren Hajiya yasa ta juya.
Har zata wuce bangaren Abdulmajid sai kuma ta karkata ta shiga.

Bayan an sanar da zuwanta, Abdulmajid dake zaune abin duniya ya dameshi yace ta shigo.
Khadija ta shiga, kallan bangarensa tai sannan a ranta tace " yafi na ya Turab kyau sosai, da ban kula da hakan ba amma yanzu na gani, ya zakai in kaji kai ba toshen gidan nan bane?"

Idanu ta kura mai tana wannan tunanin, ji tai tsananin tausayinsa ya kamata.

Batasan ma ya miko yazo kusa da ita ba, sai jitai yasa kafa ya d'an harbota.
Kallansa tai tace " Yaya."
Abdulmajid ya hard'e hannayensa ya shiga zagayeta yana kallanta yace " me ya kawoki? Ba dai zuwa kikai akan rabamu da Mairo ba?"

Hannu tasa ta riko rigarsa tace " Yaya wannan zagayen fa? Ai sai jiri ya kamani."

Murmushi yai sannan ya koma ya zauna.
Kallansa ta karayi a ranta tace " ya ya zanyi? in har kaji abinda suka maka wace rayuwa zaka shiga? Alokacin ba ka da wanda zaka gani kaji dadi, komai da kake tunanin naka ne a lokacin xakaga babu abu ko d'aya daya kasance naka, dama ace Mairo na sanshi ne....."

Khadija meye hakan?
Abinda ya fadane ya dawo da ita daga tunaninta.
Fara'a ta saki sannan tazo ta zauna kusa dashi tace " Yaya."

Ya kalleta yace " menene? Nifa na fara shakkar me kikazo dashi naga sai wani kafeni da ido kikeyi."

KAINUWA....Where stories live. Discover now