Kainuwa....90

10K 774 184
                                    

*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*LAST PAGE*

*90*

Yanda aka fito da Magajiya sai kallanta akeyi, kan kace me an cika ana zuwa kallanta labari duk ya baza akan maganin da take ba Sarki na hana haihuwa, sannan maganin da ta sama Hajiya dan kasheta, nan fa kowa ya fara tofa nashi albarkacin bakin.

Ana fitar da ita waje a ka tsaya da ita dan jiran umarnin daga sarki na asaketa.
Tahowa yai gadan gadan rike da wani makeken katako yayo kansu, kallo daya zakamai kaga bigegen d'am shaye shaye, dogarawan dake tsaye kanta kuwa suna ganin haka suka fyalla da gudu, yanda taga yayo kanta tasan tabbas sai ya maka mata, da sauri tai kasa ta tsugunna, yana karasowa kuwa ya d'aga katakon nan ya maka mata a gadan bayanta.
Ga ba baki bare ta calla kara, wani irin zakwadi na zafi ta shiga yi sai juye juye takeyi dan yauce rana ta farko da zatace a rayuwarta an mata irin wannan dukan, tsugunnowa yai inda take ya nuna ta da yatsa yace " menene damuwarki da Basira? ai na tambayi wanda ya kawoni garin nan bayan na karyamai Kafa akan wanda yasa aka kawoni shine yamin kwatance sannan naji labarin an kamaki, yau za'a yanke miki hukunci, yanzu nan da kika ganni gidan Sarkin nazo shiga kota wani hali ne dan sai naje gunki, sai naji ana cewa Magajiya, dan kut............. Dama amfani kikesan yi dani gun muzguna mata?"

Ya kara d'aga katakon zai mazga mata, da sauri ta rike kafafunsa dan ta tabbatar inya kara maka mata to fa lalai sai bayanta ya karye.
Da karfi ya fizge kafarfa sai gata a kasa ta fadi yace " kinsan masifar dana shiga bayan na mata fyaden, sam rayuwata lalacewa tai, banda shaye shaye banida aikin yi, kowa nawa ya gujeni, sannan kike kokarin jefani cikin masifa?"

Ina Magajiya ba bakin magana ga magana a ranta yana cinta, hannayenta ta hada tana bashi hakuri.
Yatsa ya nuna mata sannan yai kwafa.
A zuciye ya juya yai gaba, Magajiya sai ji tai hawaye ya zubo mata, da sauri tasa hannunta ta tabo hawayen cikin tsananin mamaki, yau itace take kuka? Ita Magajiya?

*************
A can fada kuwa Abu Turab ana fita da ita yace " Bazan maida sarautar Waziri gidan Hisham ba, sai dai zan nba babban dansa namiji wato Salihu wani mukami wanda bai kai Waziri ba."

Sannan magana ta karshe inaso kowa ya cigaba da girmama yayana Abdulmajid da bashi matsayinsa, banaso gulma akan Mahaifiyarsa ya shafeshi dan bazan yafema duk wanda aka kawo kararsa ba akan hakan."

Kallan juna sukai shida Abdulmajid, da sauri Abdulmajid ya maida kansa kasa yana tuno abubuwan da ya aikatama Turab a baya, lalai duniya abar tsoroce in ka bari santa ya shigeka to lalai kana cikin garari na rayuwa.

Sarki yana ganin haka yace " Alhamdulila komai yazo karshe, ina maka fatan alkairi ina fatan ku nacikin d'akin nan zaku bashi had'in kai kamar yanda ya kamata."

Galadima yace " Masha Allah, ba shakka komai yayi daidai, sai dai nima ina neman alfarma daga wannan lokacin inaso in ba wa Sabi'u mukamin mulkina na Galadima, ni dakai tare muka fara, haka kuma tare zamu gama, suma sai su fara a tare."

Sarki yai murmushi yace " Allah ya tayasu riko ya kuma kare mana su."
Nan akace Ameen.

Haka taro ya tashi, sai da mutane sukagama fita, Abdulmajid na kokarin fita Abu Turab yasa acemai ya sameshi a cikin falon Sarki wanda yake ta cikin fadar.

Nan Habu ya turashi zuwa falon.
Abu Turab na zaune a kasa, Sarki na kan kujera aka shigo da Abdulmajid.

Shiru ne yad'an ratsa falan kafin Sarki yai gyaran murya yace " Abdulmajid!"
Yace " Naam Ab......"
Sai kuma yai shiru, Sarki ya kalleshi sannan yace " Abu Turab!"
Turab yace " Naam Abba."
Sarki kallesu sannan yace "Abdulmajid mun yanke shawara nida Turab akan lamarinka, hakan ne yasa muka nemar maka aiki, Alhamdulila duba da matsayina da iliminka yasa ba'a sha wahala ba, dan an tabbatar min a wannan satin mai shiga komai zai kamala, anan cikin garin kaduna zaka fara aiki ba sai kayi nisa da gida ba."

KAINUWA....Where stories live. Discover now