Kainuwa....85

6.7K 601 111
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*Gaisuwa, jinjina gareku Aminan Arziki 'yan Sauyi, Dizzy, Rabes, Faty Shafi'u, Yar Gaya, Salamah, Kozali, Sharubutu, J.B, Rambi, da sauran Yan Sauyi......

*85*

A hankali ya bud'e idanunsa, sannan ya kalleta, bacci takeyi akan hannunsa na hagu, haka kawai ya samu kansa da yin murmushi, sannan ya tuno abinda ya faru jiya.

Ya akai jiya idanunsa suka rufe? Sam ya kasa controlling din kansa? Har sai da ya maidata mace? Lalai jiya yaci sa'a Bilkisu tayi wankan tsarki, da tabbas yanda yaji jiya in har bata sallah baisan yanda zaiyi ba, abu yaji wanda tunda aka haifeshi bai taba ji ba.
Lalai wannan rana ta zamar mai ranar da bazai mantata ba, murmushi yai sannan ya tuno da, a da ko zaiyi tunanin aure sam zuciyarsa bata raya mai farin ciki.

Khadija zuciyarsa take kauna kuma ya tabbata in ba dai wani ikon Allah ba bayanda za'ai ya aureta, shikuma bayaji zan iya rayuwa da wata ba ita ba, sai dai a yanzu ya tabbatar abin ba haka bane.

In har ka samu mace wacce ta sanka, sani ba wai na suna ba, sannan wacce ta ke sanka, take kokarin farantama rai, zuciyarta da kuma suffarta masu kyau ne, mai addini, to lallai shikam yana gani a hankali zuciyar mutum zata koya ma san wannan yarinyar.

Zuciyarsa haryanzu tana so da kaunar Khadija sai dai baxai taba auranta ba, saboda har abada ya tabbata bazai taba manta abinda jininta suka aikata mai ba, sannan inya hukunta iyayenta me zaice da 'ya'yan da suka haifa nan gaba in har sun tambayeshi kakaninsu na bangarenta? Kuma abu ne na sarauta wanda zai bar tarihi, ko da ya b'oye musu ya tabbatar labari zai isa har kunnensu, mai zai ce dasu a lokacin? Iyayenta sune suka...........
Motsin da Bilkisu tai da kanta shine ya katsemai wannan tunanin, kiran Sallah ake tayi a massalaci, idanunta ta bud'e cikin bacci ta kalleshi.

Ganin idanunsa a bud'e shima ita yake kallo yasa tai saurin maida idanunta ta rufe, sunkuyowa yai ya sumbaci goshinta sannan yace " zanyi alwala."
Kai ta daga mai alamar to, yace " zan dan fita daga nan kina ganin ba matsala? Naga........"
Da sauri tace " zan iya." dan batasan maganar kunya takeji.

Kanta ta zame daga hannunsa a hankali, murmushi yai bayan ya mike.
Bandaki ya shiga yai alwala sannan yai waje.

Idanunta ta bud'e a hankali bayan taji alamar fitarsa, sannan ta mike zaune, yaye bargon tai, sannan ta mike a hankali.

Dama tasa an sanar da ita duk abinda ya dace tai, yanzu zamani yazi ilimin addini ya kara wadata balle a mata tonon silili.
Bedsheet din ta yaye tai toilet, a roba ta sashi ta zuba ruwa sannan tai wankan tsarki bayan ta gasa jikinta da ruwan dumi wanda sai data dafa a heater.

Kallo d'aya zakama yanayin tafiyarta ka fahimci ba daidai take tafiya ba, bayan tayi sallah ta dade tana ma mijinta addu'a kafin ta mike.

Turab kuwa a massalaci, bayan ya gama addu'oinsa ya fito shida Garzali bayan gari yayi haske suka fito wajen gari.

**********

Magajiya kam jin an taho dashi yasa taji wani nishad'i ya kamata, gari yana haske tasa aka kira kata matan sarki.

Bayan sun zauna ne ta kallesu tace " yau munada zama na shari'a da za'ai, hakan ne yasa nakiraku dan inji ta bakinku, da Abdulmajid da Abu Turab wa kuke ganin zai gaji Sarki?"
Kallanta sukai fuskarsu da murmushi sukace "Abdulmajid mana."

Tace " ba sai na tsaya bata lokaci na ba tunda kunsan abinda ya kamata, ina fatan zaku bi bayana anjima."

Kallan juna sukai kafin su amsa da to, suka taso suka fita, suna fita d'aya tace " matar nan tana neman maidamu yaranta, da izinin Allah d'an datake takama dashi bazai zama sarkin ba."
D'ayar tace "Ameen."

KAINUWA....Where stories live. Discover now