Kainuwa.......17

7.8K 458 6
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🤸🏼*

*17*

Itama Magajiya a daren ta shirya taje ta samu mai martaba da nata sharad'in, yayi mamaki kwarai dajin wannan zancen, ya kalleta harzaiyi magana sai ya fasa yace " shikenan ya amince, hakan datai ya nuna masa lalai ba zaman amana take dashi ba haka kuma ta nuna d'ansa ba nata bane."

Magajiya ta juya kai bata ce komai ba dan itakam a yanzu abu d'aya kawai ta sani wato ta tabbatar ta d'aura d'anta a mulki ba komai ba.

Haka mai martaba ya rubuta mata a takarda ya kalleta cikin takaici sannan yace "na dauka na sanar dake d'ana yana da lalura?"

Bata amsa mai ba ta dai amshi takardar hannunsa sannan tai murmushi tace " ba wai rashin yarda ne ko rashin san d'anka bane yasani yin haka sai dai nayi haka ne saboda kauda matsala dazata iya afkuwa nan gaba, me zai faru idan nan gaba ka tara 'ya'ya anzo ana takara da kishi akan mulki? Amma kaga in har mun riga mun tsaida babban d'a a matsayin magajinka banaji wata babbar matsala zata faru."

Kallan yai cikin mamaki duk da dai maganarta ba karya bane sai dai yana ganin sankai da san mulkinta ne yasata yin haka, yafi kowa saninta ya san abinda take tunani, tana tsoro kar nan gaba yaron ya warke in fara tunanin sashi a mulki.

Sallama tamai ta fita.

************

Washegari wajen sha biyun rana aka turo da mota dazata daukesu.

Kofar gidan sarauta aka bud'e, Abu Turab ya kurama kofar ido yana kallo, gannin tsari da girman gidan yasa ya shiga kalle kalle, mamaki yakeyi duk wannan katan gidan na mahaifinsa ne?

Basira ce ta tabashi, ya juyo ya kalleta hararar sa tai sannan ta nuna mai sandarsa, da sauri yai kasa da kansa sannan ya d'auki sandar.

Sun sauka Lantana ta kama hannunsa suka nufi b'angaren da wata baiwa tazo dan nuna musu.

Ba b'angaren ta na da bane wannan yafi girma saboda an warema Abu Turab nasa bangaren.

Haka akai ta zuwa ana gaidasu wasu gaisuwa sukazo, wasu kuwa gulma sukazo, wasu kuwa so suke suga lalurar da yaron ke dashi.

Kafin kace me? Zance ya baza gidan akan Abu Turab makaho ne.

Abdulmajid kam yana gun Magajiya tana kara huremai kunne akan karya kuskura ya bari yaron nan ya rainashi, dan nan gaba baisan mai zai zamar masa ba.

Sun dade a d'akin kafin tace ya tashi ya koma bangarensa.

Abdulmajid nada tsananin kishi, jin akwai wani d'a bayanshi a gun Mai Martaba yasa ransa ya bace, kallan masu kula dashi yai yace " muje in ga kanin nawa."

Haka ya taho dan ya matso yaga kanin nasa da sam baya farin cikin kasancewarsa, sannan yanasan yagani in da gaske baya ganin.

*******

Abu Turab na xaune aka dinga shigowa da kaya, sai dai ba dama ya nuna yana gani, kansa ya kawar gefe yana wasa da hannunsa, sun ajiye kaya dayawa daga na sawa, takalma da sauransu, sannan suka gaidashi.

Juyowa yai inda suke ya amsa tare da cewa "su waye?"

"Mai Martaba ne ya aikomu mukawoma kayan sawa, sannan ga abinci kala kala ya sa a girkama, yace a sanar dakai xai turo anjima a kaika gunsa."

KAINUWA....Donde viven las historias. Descúbrelo ahora