Kainuwa.....73

6.6K 567 68
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*73*

Ta gabansa ta wuce a zuciye tai waje.
B'angaren Turab ta nufa, ba kowa a bangaren sai mai kula da kofa, gaisheta yai ya sanar da ita ai ba kowa a nan.
Juyawa tai hankalinta a tashe, ina ya kaimata d'anta? Itakam mai makon wannan ranar ta zama ranar farin ciki yau kam wannan ranar ta gama zame mata ranar bakin ciki.

Ga magrib ta kawo kai.....

***********

Duk yanda Khadija taso da ya bud'e ido amma inaaa, ya kasa,yana kwance idanunsa a rufe, itakam gani take kamar baya haccinsa, sai dai shikam bayaji zai iya bud'e idanunsa yaga maike faruwa a wannan duniyar, bayasan ya bud'e idanunsa yaji abinda kwakwalwarsa bazata iya d'auka ba.
Khadija zama tai a gabansa duk ta rame a 'yan kwanakin nan dan itakam sam yanzu rayuwar bata mata dadi, tace " Yaya ka taimaka ka farka."

A can gidan Barde kuwa kwance take a kan gado banda juyi ba abinda takeyi, ta rasa menene ya hanata bacci, ta dade tanata juyi ta gaji ta mike zaune tare dayin dogon tsaki tace " Allah ya isa? Wannan wace irin muguntace? Haka kawai ku samu mutum ku hau dukansa ba gaira ba dalili?"

Ahh ashe fa akwai dalili tunda Ya Turab akaje daka shi kuma ya shiga motar?
Hannu tasa akan kirjinta tare da turo baki gaba tace " Allah sarki, ashe mutumin nan nada tausayi, sannan zuciyarsa ba wai mara kyau bace duka, me yasa muka kasa gani?"
Ajiyar zuciya tai ta tuno sanda take mai rashin mutunci shi kuma yake nuna ba komai, batasan sanda ta sa murmushi ba, tunowa datai yanda ta ganshi a kan gado yasa jikinta yai sanyi.
Idanunta ne taji ya ciciko, da sauri ta kwanta taja bargo ta rufe duka har kanta.

***********

Mai Martaba ne ya kalli Turab yace " ya akai Abdulmajid ya kasance cikin wannan halin?"
Turab ya kalli Abdulmajid da ke kwance yana bacci, karfe shida da rabi ne na safe dan ana sallar asuba suka taho shida Mai Martaba.
Khadija na kwance akan sallaya rike da karamin kur'ani izu biyu da alama tana karatu bacci yai gaba da ita.
Yace " Tuba nake ranka ya dade amma ni akaso halakawa."
Sarki ya kalleshi yace "Shi kuma yaji kenan?"
Turab ya d'aga mai kyai.
Idansa ya runtse kadan sannan ya juya.
Turab yace " Abba bazaka shiga ba?"
Kai ya girgiza yace " kana tunanin zaiso gani na? Ko kana tunanin zai so ganin kowa? Bayan yaji da kunnensa mahaifiyarsa na neman yin kisan kai? Me kake tunanin yana ayyana wa a kwancen nan da yake?"
Turab ya kalli Andulmajid cikin tausayawa.
Sarki ya kamo hannun Turab yace " Abu Turab!"
Turab ya kalleshi sai dai bai amsa ba.
Sarki cikin wata irin murya yace " na girma, sannan ko ban girma ba haka na taso a rayuwar auranmu da barin Magajiya taci galaba akan dukkan lamuranta, saboda bata taba barin evidence dazai nuna tabbas itace ta aikata abu, sannan inba wanda ya san halinta ba ba wanda zai yanda akan abin da zata iya aikatawa, ina rokonka daka taimakama wannan mahaifin naka ya aiwatar da babban harkar shari'a ta gaskiya na karshe akan gadon mulkinsa, ka kawomin hujjojin da zasusa Magajiya ta fuskanci hukunci akan mayyan laifukan da ta aikata, wannan shine babban burina da ya ragemin a duniya in hakan ta faru inaso inyi murabus in baka mulkin nan, in d'auki mahaifiyata da matata mu ziyarci ka'aba dan ziyarar d'akin ma'aiki sannan mu jira sanda in karasa rayuwata cikin al'umma ina kallan yanda kake tafiyar da naka mulkin wanda shine abinda nafisan gani."

Turab yai shiru yanajin kalaman mahaifinsa,can ya d'ago yace " Abba insha Allah wannan d'an naka bazai baka kunya ba, sai dai maganar murabus mayi daga baya in komai ya kamalla."

Sarki yai murmushi sannan ya kara kallan Abdulmajid cikin tausayawa sannan yai waje.
Turab ne ya murd'a d'akin jinshi a kulle ya kai hannu zai kwankwasa.
Yanda yaga khadija tana bacci ne yasa ya sauke hannu tare da fasawa, ya tabbatar tana bukatar hutu.

KAINUWA....Where stories live. Discover now