Kainuwa.....29

6.1K 500 36
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*29*

Khadija bangaren Magajiya ta isa, tana shiga ta taddata a zaune, karasawa tai ta gaisheta, Magajiya ta kalleta cikin kulawa tace " Khadija sannu, ina nan hankalina a tashe ina tunanin yanda jikinki yake, Khadija ya akai haka? Duk kin rame."
Khadija ta d'ago ta kalleta bata bata amsar tambayarta ba sai jitai tace " Umma an tura wani ya dubo Inna Lami?"
Magajiya tad'an tabe baki kadan sannan ta kalleta tace " na tura, sunce jikin da sauki."

Hawaye ne ya zuboma Khadija tace " Umma me yasa bakwasa tausayi a ranku?"
Hade rai Magajiya tai tace " KHADIJA!"
Khadija tana kuka tace " makociyar Inna Lami ba ta aiko a sanar daku jikinta yayi tsanani ba?"
Magajiya tace " a yaushe akai hakan?"
Khadija tace " amma tace ai ta sanar da Yaya, Umma Allah ya d'auki ran Inna Lami, ita kanta bata sani ba tunda ita tasan ta sanar da Yaya ta dauka anje an dauketa, ita kuma a ranar tai tafiya, sai jiya da ta dawo ta shiga gidan ta ganta duk ta kumbura da alama ma ta dade da rasuwa, nan tasa aka kira mutane aka mata sallah aka kaita, d'azu da naje take sanar dani......"

Kukanta ne ya tsananta sanda tazo karshe.
Tace "Umma Inna Lami fa kanwar Mahaifiyar ku ce, tayaya zaku..."
Ya isa haka!
Abinda Magajiya tace kenan, d'agowa Khadija tai ta kalleta, dan tayi maganar ne da kakkausar murya.
Magajiya tacigaba " Ya isa haka Khadija, Inna Lami ta rasu Allah ya jikanta, zansa aje gidan, ke kuma jan maganar ya isa, ba kuma na san ki kara tada maganar nan."
Kallanta Khadija ta shiga yi cikin tsananin mamaki, Magajiya ta kalleta tace " ki tashi ki koma gida zan aiko miki da magani da abubuwan bukata, banasan ki dinga kwanciya ciwo akan abinda bai kai ya kawo ba."
Sam ma ta rasa me zatace sai kallan mamaki kawai datake binta dashi.
Ganin batada niyyar kara magana yasa Khadija ta mike ta fito daga d'akin.
Ba shakka yau taga abin mamaki ace d'an uwanka na jini? Sannan harda wani wai batasan taga tana kwanciya akan abinda bai kai ya kawo ba? Kenan abinda sukama Turab da wannan rashin kula da Inna Lamin da sukai ba wani abin bane a gunsu?

Samun kanta tai kawai da bin hanyar da zata kaita gun Abu Turab.
Sai dataje kofar shiga ta tsaya tana tunani me zatace mai?
Tabbas ganinsa ne kadai zaisa taji saukin wannan abin.
Tura kofar tai a hankali, Mai kula da gun ne ya taso ya gaisheta, a hankali ta furta Ya Turab nanan?
Yace " eh yana ciki, a sanar mai da zuwanki?"
Tace " bari na shiga ai kasan ni ko?"
Kallanta yai yace " na sani amma taya....."
Gani yai kawai tayi gaba batama san yanayi ba.
Falo ta duba ganin bayanan yasa ta tsaya taba kallan falon, idanunta ne suka kara zubo da wasu kwallar sannan a hankali ta nufi kofar d'akinsa kwankwasa wa tai daga ciki yace " waye?"
Shiru tai sai kuma ta kara kwankwasawa.
Mikewa yai ya bud'e kofar.
Kallanta yai sannan yai saurin kauda kai ya kara cewa " waye?"
Kallansa ta shiga yi hawaye na zubo mata, a zuciyarta tace "Yaya ina cikin wani hali, su Umma Magajiya, Yaya, da Abbana sun fara bani tsoro, banaji suna da digon tausayi a zuciyoyinsu, Yaya ya zanyi in canza su? Ya zanyi in nuna musu hanyar gaskiya?"
Hawayenta ta shiga sharewa, jiyai zuciyarsa na kuna ya tsani yaganta tana kuka, gashi yaga ta rame sosai da alama rashin lafiya tai, daurewa yai ya juya da nufin komawa ciki, jiyai tace " nice Yaya."
Juyowa yai yace " Khadija? Me kike a nan?"
Ta daure tace " ganinka kawai nazoyi, ya hannun naka?"
Fuska ya had'e yace " me zaisa ki damu da ciwon da baikai ya kawo ba, bayan kece kike bukatar kulawa?"
Daurewa tai tace " yaya ya warke?"
Labansa yadan ciza yace " Khadija meke damunki? Me yasa bakya fahimtar abinda nake nufi? Kina tunanin in kika nuna damuwarki akan ciwona kika wulakanta naki lafiyar zanji dadi? Me yasa kike san ki dinga sani cikin damuwa?"

Kallansa tai fuskarta cike da mamakin kalamansa, tace " Yaya."
Idanu ya d'an runtse yace " please in har kinasan ki nuna kulawarki a kaina to ki kula da lafiyarki."
Juyawa yai ya koma ciki, ya rufo kofar.

Shiru tai sai hawaye da suke zubowa daga idanunta, jingina tai da jikin kofar, shikansa yana shiga ya jingina da jikin kofar.
Idanunta a lumshe tace " Yaya."
Bai amsa mata ba sai dai yana jinta, tacigaba " Kayi hakuri yaya, kayi hakuri da rashin sanar dakai tafiyata fa banyi ba, kasan ina zaune a gunka lokacin da aka aiko inje, ina zuwa aka sani a mota ko gida ban shiga ba, kayi hakuri da rashin nemanka dabanyi ba, tunda naje garin ba'a kara barina na zo ba sai wannan dawowar."
Iska tadan furzar sannan tace " Yya kayi hakuri na abinda su Umma Babba sukama, sannan kayi hakuri na rashin baka hakuri da sukai."

Ransane ya bace ya bud'e kofar da karfi, hakan yasa tai saurin gyarawa ganin ta kusa faduwa, a fusace yace " meyasa kike bada hakuri? Me kikai? Me yasa kike bada hakuri a koda yaushe? Bayan wadanda ya kamata su bada hakurin basusan ma sunyi laifi ba? Me yasa Khadija? Meyasa kike neman tadamin hankali?"
Kai ta shiga girgizawa har ya gama fadan sannan tace " Yaya na san....."
Katseta yai yace " Khadija meyasa bazaki fahimceni ba? Banasan kina yawan bani hakuri hakan na sa inji kamar nine nake miki laifi."

Daurewa tai tace " Nadaina yaya."
Yace " Khadija please....."
Murmushi ta kakaro tace " na daina Yaya, nazo ne dan ina cikin wani hali zuciyata bata kawo min kowa ba sai kai, shiyasa nazo."

Kallanta yai yace " me ya sameki?"
Murmushi tai tace " hmm inama Yaya kana gani? Da kaganni ina ma murmushi."
Shiru yai baice komai ba, tace " Haryanzu addu'ata kenan, Allah ya bud'ema idanunka."
Murmushi taga yayi, itama murmushin tai sannan tace " Ahh da alama zuciyata tayi sanyi,duk da hankalina haryanzu bai kwanta ba."
Yace " me ya faru kuma?"
Tace " Inna Lami ta rasu."
Yace " yaushe?"
Kallansa yai tace " ba'a san yaushe bane."
Kallan mamaki ya mata, ganin zata d'ago yasa ya kauda kai yace " ban gane ba."
Zama tai a kasa a jikin bango, ta kama rigarsa tace " Yaya zauna plz."
Zama yai dan ya kula tana bukatar mai lalashi."
Zayannemai komai tai.

Hankalinsa ya tashi, lalai mutanen nan basuda imani, wato abin ma harda jininsu?
Khadija ta d'ora da cewa " Yaya in kaine me zakayi?"
"Hmmm in nine ba abinda zanyi."
Tace " ba abinda zakai?"
Kai ya d'aga alamar eh yace " me zanyi to? Abin nan dai ya riga ya faru, sannan mutanen na basu nuna tausayawa ko dana sani ba, ni da nake d'a me kike tunanin zanyi? Sai dai...."
Shiru yai hakan yasa tace " sai dai me?"
Yai ajiyar zuciya yace "sai dai dole girma da darajarsu zai ragu a idona."

Tace " na fahimceka Yaya na kuma gode."
Mikewa tai tace " yau naji dadin dana dade banji ba duk da wata zuciyar tana tausayawa Inna Lami, sai dai wata zuciyar tana farin cikin zama tare da kai danai wanda na dade ban samu ba."
Baice komai ba, tace " nagode yaya."
Ta fada tare da tafiya.
Kallo ya bita dashi sannan ya mike a hankali ya koma ciki.

Ya zaiyi? Ya zaiyi? Ba shakka yanasan Khadija sai dai yana ganin auransa da ita ba mai yiwuwa bane, tsanar Magajiya da ahalinta ne suka kara shigarsa jin labarin da khadija ta bashi.

Kansa ya dan shafa yace " Ya zanyi?"

*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*

KAINUWA....Where stories live. Discover now