Kainuwa...47.

6.4K 487 24
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*47*

Duk yanda taso ta danne zuciyarta ta kwanta ta kasa, mikewa tai ta zura alkyabbarta sannan ta kalli Mai kula da ita tace " yau kwanan waye?"
Kasa tai dakai tace " naki ne ranki ya dade."
Magajiya ta d'an d'aga gira sama sannan tace muje inasan ganin me martaba.
Tayi mamaki sosai dan rabon da Magajiya taje turakar mai martaba da niyar kwana har ta manta.

Haka suka fito suka nufi b'angaren Mai Martaba.
Sunje shiga soro bangaren nasa sukaji ana gulmar Abdulmajid da Mairo, d'ayar tace " wlh jakadiya ce ta gansu da idanta yar gidan Barden ta fito daga b'angaren Yariman."
Magajiya ta cusa kai suna ganinta suka rude a tsorace suka tsugunna sukace " Barkanki da zuwa Magajiya."

Kallansu tai fuskarta dauke da iza tace " ina san dukanku kuje bangarena ku jirani, kada kuma ku manta a tsaye nakeso kuntsaya har na iso."

Kara runkufawa sukai suna neman bada hakuri, wani kallo ta musu da ya sa sukaja bakinsu sukai dif.

Nan suka karasa ciki.
Jakadiya ce ta fito da sauri kana kallanta zaka gane abinci takeci ta taso.
Wani banzan kallo Magajiya ta mata, da sauri tai rusuna tana gaisheta.
Magajiya bata amsa ba sai alamu da ta mata na ta mata iso.
Mikewa tai ta nufi b'angaren Sarki.

Rubuce rubuce yake tayi, yana jin sallamar Jakadiya yai saurin had'e takardun nan ya sa a kasan carfet din da yake kai.
Jakadiya ta shigo ta gaisheshi sannan ta sanar mai da zuwan Magajiya, alama kawai ya mata da kai akan ta shigo.

Magajiya ta shigo ta zauna a inda ta saba zama, sannan ta kalleshi tace " Barka da dare Haikawa."

Sarki ya amsa sannan yace " lafiya dai da daddaren nan?"

Tace " ina tunanin yau kwanana ne? Banaji na cancanci inji wannan kalmar daga bakinka."

"Kwana? A tun wani karnin kenan?"
Murmushi tai sannan tace " Turab na garin Kano ko?"
Kallan ta yai sai dai bai amsa mata ba, a ransa yace abinda ya kawoki kenan?"
Murmushi ne ya bayyana a fuskarta tace " na yaba da d'ana Turab ba shakka yanada hazaka da tunani, ina kuma kara godemai da maganin da ya bani."

Sarki ya jinjina kai yace " ai dama hakkin d'a ne ya kula da uwarsa, in har ita uwar tana neman cutar dashi to shi ya kamata ya nuna mata yana santa."

Kura mai ido tai dan tasab magana yake gwab'a mata.
Isakar ta d'an firzar kadan tace " haka ne, sai dai inaso uban d'an ya cigaba da nunama d'an nan hanyar dazai kula da mahaifiyar tasa."

Murmushi Mai Martaba ya saki tare da d'an juya kai kad'an harzaiyi magana sai kuma ya fasa.
Kallansa tai dan fuskarta cikin fara'a tace " yaushe zaka yima babban d'anka mata? Dan na tabbatar kanada babban buri akansa shiyasa ka kasa yimai cikin gaggawa
"
Ya fahimci me takesan cewa hakan yasa yace " ni ai danayake na d'aura buri akansa shiyasa nai tunanin barinki ki nemomai mata."

Fuskarta ta tsuke dan tabbas taji haushin maganarsa.

Takarda ta d'auko ta taso a hankali tazo ta ajiye mai agabansa.
Kallan takardar yai yace " na menene?"
Tace " tuni nake maka akan rubutu dakai na cewa Abdulmajid ne zai gajeka."
Fuskar shi ya d'aure yace " sai akai yaya kuma?"

KAINUWA....Where stories live. Discover now