Kainuwa...89

5.9K 517 57
                                    

*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

* SECOND TO D LAST PAGE*

*89*

Bilkisu tace " Mairo menene tsakanin shi da Khadija?"
Mairo tace " menene kuwa, zumunci ne na ya da kanwa kamar ni."
Bilkisu ta kura mata ido, da sauri Mairo ta mike tace " bari naje gida naga yamma tayi."
Kafin Bilkisu tai magana tayi wuf tayi waje.

""*******""""
Gimbiya ta dade a zaune tana tunani kafin ta mike ta shiga d'aki, tana shiga ya turo kofar tare da sallama.
Juyowa tai ta kalleshi tare da amsamai.
Karasowa yai inda take kawai sai jitai ya rungumeta tsam a jikinsa a hankali yake fitar da wani numfashi, murmushi tai sannan tasa hannu ta shafi bayansa tace " Weldone dear."

Sun dade makale da juna kafin ya d'ago tare da rike kafad'unta yana kallanta.
Wani sansanyan murmushi tamai tace " ya akai?"
Yace " jikinkinfa?"
Tace " na ware, sai kadan"
Ya kara rungumeta yace " Sannu, yau nasan kinsha wahala."
Tace "kaine kasha wahala, ni me nai? Ya hakurin mu? Ni ko ganin Hajiyar ban taba yi ba,Allah bai nufa ba."
Yace " Hajiya ta girma sosai wanda kowa yake mata tunanin mutuwa, sannan dan rashin imani matar nan ta nemi halaka mata rayuwa ba tare da tayi duba da tsufanta ba."
Bilkisu tai shiru, jiki a sanyaye.
D'agowa yai tare da kama hannunta suka zauna a bakin gado, kwanciya yai tare da d'aura kansa akan cinyarta yana kallanta yace " Kinji abubuwa na tashin hankali da mamaki yau ko?"
Hannunta tasa akan sumarsa tace " a'a, ni duk abinda ya faru abu d'aya yafi tadamin hankali, ganinka danai cikin wani yanayi kana neman fita hayyacinka."
Yace " abinda Magajiya tai fa?"
Tace "Magajiya? Hmm ko kad'an ban tsorata da ita ba saboda na tabbatar in har hankalinka da ta nemi gusarwa ya dawo to tabbas komai zai daidaita, sannan zaka juya kan akalar muguntar da ta shirya."
Murmushi ya mata sannan yace " Thanks alot for believing in me."
Tace " nima Thanka alot."
Yace " ke kuma for me?"
Tace " bakasan abinda yafi komai min dadi ba?"
Yace "a'a"
Tace " yanda nima ka yarda dani kake kuma sanar dani damuwarka."

Murmushi ya mata yace " ni kaina har yanzu ina mamakin yanda ke kadai zuciyata ke iya bod'ewa damuwarta."
Tace " ina rokon zuciyarka da ta kara sanar dani d'amuwa d'aya da na ke san ji."
Kallanta yai yace " name kenan?"
Kallansa tai sannan tai kasa da idanunta a hankali ta furta Khadija!"

Kallanta yai sannan ya mike daga kan cinyarta ya zauna yace " Khadija?"
Juyowa tai ta kalli kwayar idanunsa.
Mikewa yai hannu tasa ta riko hannunsa da sauri tace " Yarima."
Tsayawa yai sai dai bai juyo ba, tace " inada tsananin kishi hakan ne yasa nakesan na auri wanda yake sona sosai, sai dai duba da yanayin gidan dana fito nasan tabbas Mahaifina bazai bada ni ba sai ga wani mai matsayi na sarauta, sannan nasan Sarki bazai taba zama da mace 'aya ba, in har ka b'oyemin tsakaninku shine zai sani jin ba dadi a raina bawai shirunka ba."

Turab ya juyo ya kalleta sannan ya sakar mata murmushi yace " Later, zan sanar dake komai amma ba yanzu ba, banasan wani abu ya shiga zuciyarki a wannan lokacin, zan sanar dake in har kika sake tambayata, sai dai ba wannan lokacin ba."

Murmushi tai tace " nagode sosai."

Kusa da ita ya matso ya rikota jikinta.
Sai da sukai sallar isha'i sannanya sanar da ita hukunci sarki da kuma abinda suka yanke akan Abdulmajid sosai ta yaba da shawarar da suka yanke.

A ranar uku kuwa Mai Martaba Sarki ya tattara mutane ya sanar dasu hukuncinsa, sannan dama ya riga ya hana mutanen dake d'akin zancen Abdulmajid.

KAINUWA....Where stories live. Discover now