Kainuwa....82

6.8K 562 49
                                    

*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*82*

Bayan tayi sallar magrib ta yafa mayafinta katon gaske, lulubi tai sosai da sosai, wanda inba kaga fuskarta ba bazaka taba cewa Magajiya bace, ta fito, tara bayinta tai ta sanar dasu zata fita sai dai batasan kowa yasan ta fita sannan ko anzo nemanta a tabbatar ance tana bacci.

Ita kadai ta fito ta nufi inda aka killace Hisham.
Tana zuwa ta sauke mayafinta sannan ta kalli masu tsaron gun tace "yana ciki?"
Kallanta sukai bayan sun gaisheta sukace " Ranki ya dade Sarki ya umarcemu akan kar kowa......."

Wani kallo data buga musu shine ya hana su karasa maganar, tace " nice kowa?"

Da sauri sukace " ba haka bane......"
"ya isheni, bud'e."
Jikinsa na rawa ya bud'e kofar ta shiga."
Hisham na zaune ya had'a kai da gwiwa saboda abin duniya da duk ya taru yamai yawa, ba shakka yana cikin tsaka mai wuya.
Ta window ta tsaya tace "Yaya!"
D'agowa yai ya kalleta, ba shakka wannan itace wacce ta ruguzamai rayuwa, dan itace ta kawo shawarar d'aura d'ansa akan mulki wanda hakan ne yasa ya bata d'an ba tare da yin wani dogon nazari ba, sannan wannan shine dalilin daya sa sam idanunsa suka gama rufewa yakejin koma meye zai iya zuciyarsa ta zarme indai akan hawan d'ansa mulki ne to tabbas zai iya koma menene.

Kallansa tai cikin zafi tace " magana nake."
Mikewa yai ya iso inda take, kallanta yai yace "ya akai?"
Tace " baka tambayeni jikin d'anka ba?sai kacemin ya akai?"
Kallanta yai yace " d'ana? Bayan kece kika hana wannan maganar?"
Tace " yaya ai duk hanawar danai jini ai jini ne, sannan karka damu da gida, zan kula dasu kamar yanda zan kula da kaina, kai dai ka kara hakuri."
Kallanta ya sake yi yace " me ya kawoki? Dan na tabbata bazaki taso nan ba bayan kinsan abinda ke faruwa kizo nan ba tare da kwakwaran dalili ba."

Tace " Yaya ka san kome nakeyi a yanzu saboda Abdulmajid nakeyi ko?"

Kallanta yai dan yama kasa magana, tace "yaya karka damu da duk abinda ke faruwa, koda wani abun ya sameka ni ina nan, sannan in har ina duniya tofa kamar kai kana cikinta ne, d'an mu da 'yayanka ni na d'au alkawarin rikesu amana......."
Katseta yai da cewa " me kikazo fad'amin."
Juyowa tai ta kalli waje, can ta hangoni rakube jikin window rike da takardata da birona, kallo d'aya ta sakarmin na fita a guje kamar wacce aka biyo da wuka, dan tabbas na tsorata, wannan dalilin yasa sam Bansan me tace masa ba.

Sai dai tana gama maganarta na kalli Hisham, kallan da Hisham yake mata kadai zaka kalla ka tabbatar da lalai shi kansa yasha mamakin kalamanta.
Kallansa tai tace " Yaya bansaka dogon tunani ko dogon nazari ba dan abinda na sanar maka shi za'a aikata indai kana san kanka da lafiya, ni kabarni da waccen yaran, kai dai kayi abinda ya dace."

Yama kasa magana sai kallanta da yakeyi, tace "ni na wuce, ina kuma jiran ganin abinda nace."
Ta juya ba tare da taji asarsa ba.

Tsananin mamaki kawai yake, sai binta da kallo kawai da yai.
Tana fitowa ta ciro abu a jikinta ta mikama masu kula da kofar tace "waye ya ziyarci Waziri?"
Da sauri sukace " ba kowa ranka ya dade."

Juyawatai tai gaba abinta.

Tana shiga bangarenta cikin d'aki ta yaye mayafin ta shiga zirya a d'aki, Hisham zaibi abinda tace? A fili tace dole ne ai.

Ya zatai in bai bi ba?? Kai take girgizawa da sauri in zuciyarta ta nemi kawo mata wannan tunanin, sai tace innaaaa....."

*******
Basira kuwa da yama ta wuce gidan dan Turab dashi da Garzali ne sukazi suka rakata, hmm Umma anga Lantana.

Nan suka shiga hirar yaushe gamo bayan ta dan zauna gun hajiya ta dubata da jiki.

KAINUWA....Where stories live. Discover now