Kainuwa......18

6.9K 445 41
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*18*

Lantana ce ta zo ta daukeshi tai b'angarenshi dashi, akan gado ta kwantar dashi har lokacin bata daina zubar da hawaye ba, bargo yaja ya luluba ita kuma ta mike ta fito.

A tsaye ta taradda Basira, kusa da ita taje ta tsaya ba tare da tace komai ba.
Basira ta juyo tace " yana ina?"

"nakaishi d'aki." ta fad'a tare da kara share kwalla, Basira ta had'iyi wani yawo na takaici sannan tace " ki amso mai magani yasha."

Tace to, sannan ta juya ta fita.

*********

Mai Martaba kam ana la'asar ya kalli Barde yace " a aika a kira Abu Turab."

Barde ya kalleshi jiki a sanyaye yace " Takawa kayi min afuwa amma ina ganin ka bari sai zuwa wata rana sannan a nunashi a fada." a hankali yai maganar.

Mai Martaba yasan halin Barde tunda ya fadi haka da alama akwai wani kwakwaran dalili, hakan yasa bai sake magana ba.

Ana tashi daga fada ya tambayi Barde abinda ke faruwa.
Barde ya nisa yace " bansan nikaina takamaimai menene ba sai dai naganshi ya taho gunka sai kuma ya juya."

Cikin mamaki Mai Martaba yace " ban gane ba?"

Nan Barde ya sanar dashi abinda ya gani.

Hankalin Mai Martaba ne ya tashi sosai nan ya juya afusace yai bangaren d'an nasa.

Bai jira Zagi ya isar da zuwansa ba ya fada ciki da sauri.

D'akinsa ya nufa ya bud'e, a dukunkune ya ganshi cikin bargo, da sauri ya karasa gunsa ya d'agoshi.

Jikinsa zafi rau wanda hakan ya kara tadamai hankali, ya kalli Abu Turab wanda idanunsa sai lumshewa suke, yace " Menene? Waye ya tabaminkai? Har yajama zazzabi?"

Kai Abu turab ya girgiza alamar bakowa.

Fuskarsa yace " bayin dana aiko da kayanka sune suka baka yagagge ko akwai wani abun?"

Abu Turab jiyai wani kuka yazo mai, baisan sanda yasa kuka ba, kuka ya shigayi sosai.

Mai Martaba ya rungumeshi tsam a jikinsa hankalinsa a tashe.

Abu Turab ya dade yana kukan sannan ya share hawayensa cikin murya mai raunin gaske yace " kayi hakuri na tadama hankali daga zuwana."

D'ago dashi yai ya kalleshi yace " ni zan baka hakuri na rashin kula da abinda ke faruwa dakai."

Abu Turab ya share kwalla baice komai ba.

Yana zaune kusa dashi har bacci ya dauke d'an nasa sannan ya mike ya fito.

Bangaren Basira ya shiga, zaune ya ganta tana cin abinci.

Sai daya zauna sannan ya kalleta yace " Abu Turab yaci abinci ne?"

Murmushi tai tace "in bashida lafiya bayacin abinci dan ko yaci zai dawo dashi."

Ya kalleta ya kalli yanda takecin abinci yace " Basira mai ya sameshi? Ance ya sa kaya bayan rigar a yage."

Abincin hannunta ta ajiye dan dama ci kawai takeyi, ta kalleshi tace " bansan me ya faru ba nima na dai san bashida lafiya."

Ido ya kura mata, tai saurin kauda kanta gefe, yace " wanene yamai haka? Na tabbata kinsani."

KAINUWA....Where stories live. Discover now