Kainuwa....62

6.7K 533 36
                                    

*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*62*

Khadija tana fita ta samu guri a waje ta xauna, jitai jikinta duk ya kaure da rawa, ba shakka wannan ce rana ta farko da tai tafa kukewa tai ma wanda ya girmeta magana irin haka, balle Magajiya mace mai tsananin kwarjini da mulki.

Mikewa tai a hankali, so take ta samu Abu Turab taji a wani mataki na aure ya d'auka tsakaninsa da Mairo? Dan ba shakka tana san d'an uwanta ya aureta ko dan ranar da wannan sirri ya bayyana ya zama akwai wanda zai gani yaji dadi, ta tabbata in tai magana gani za'ai kamar kishi ne ke damunta sai dai ko d'aya, tasan akwai kishi na wanda take tsananin so shikuma ba ita yake so ba, sai dai a yanzu burinta tai kokarin ganin ta gyara wani abu ko yaya ne na daga cikin laifukan da aka aikata.

Bangarensa ta nufa, har takai hannu zata kwankwasa ta fasa saboda batasan da wace kalmar zata fara masa magana ba, a hankali ta juya cikin damuwa.

Idanu ta zaro, kallanta yai sannan ya kalli kofar, miyau ta had'iya sannan tace " Ya Turab."

Kallanta ya sakeyi sannan yace "Lafiya?" daga bangaren Hajiya yake sam bayasan magana.

Khadija tai shiru tana wasa da hannayenta, tunanin abinda zata cemai takeyi.
Ta gefenta ya wuce zai shiga ciki ganin batada niyyar magana.
Itama ganin haka yasa tai saurin cewa "Magana nakeso muyi."

Juyowa yai ya kalleta sannan ya kauda kai yace "Banaji akwai wata magana da zamuyi."

Kasa tai da kai tare da jinjina kai cikin rashin jin dadin abinda ya fada tace " haka ne, na tabbatar ba wata magana datai saura tsakaninmu, sai dai inaso ka bani ko minti goma ne."

Harshensa ya zaro kadan ya d'an lashi lab'ansa da suka bushe yace muje.
Mai makon yai ciki sai taga ya juya ya fara tafiya.

Bata tambayi inda zasuba itama binsa kawai tai a baya.
A hankali suke tafiya yana gaba daga gefen dama, ita kuma tana bayansa daga gefen hagu, tafiya kawai yakeyi. Yana kara tattaro duk wani tugu da ya sani wanda Magajiya ta aikata ita da yayanta wanda ya kasance mahaifin yarinyar dayafiso a rayuwa.

Ta yaya zai iya zaman aure da ita ko bayan komai ya kamala? In har ya sa akama mahaifinta da Magajiya hukunci ta yaya zai iya kallanta da sunan soyayya? Itama ta yaya zata iya kallan wanda ya ruguza rayuwar gidansu da sunan soyayya? Ai duk san da takemai bai kai na iyayenta ba, shima haka, duk sanda yake mata bazai taba kwatanta shi da wanda yakema mahaifiyarsa ba.

Juyowa yai ya kalleta, ganin irin kallan da yake mata yasa jikinta yai wani irin sanyi.
Baice mata komai ba sai nuna mata inda zasu shiga dayai.
Kallan gurin tai, inda ya ke hutawa ne, sai daya shiga ta bi bayansa.
Can yaje ya zauna akan kujerar dake gun.
Rasa inda zata zauna tai dan kujerar gud'a d'aya ce a gun doguwa.
Kallanta yai sannan ya mata alama da kai akan ta zauna daga gefe.

Nan ta zauna, ta d'an kalli sararin samaniya, kasancewar yamma ce garin yayi luf abin sha'awa, bare lokacin na zafi ne, iska tana kad'awa a hankali.

Jitai yace " ina jinki."
Khadija ta kalleshi kallo na tsananin kauna, inama lokacin da suke yara ya dawo? Lokacin da suke kullum tare, cikin tsananin bege da kulawa.

Kin kafeni da ido bakice komai ba.

Khadija ta kakaro murmushi tace " Ba fara'a yanzu a tsakaninmu."
Kallanta yai sai dai baice komai ba ya maida kansa inda yake kallo da.

KAINUWA....Where stories live. Discover now