Kainuwa.....10

6.6K 495 50
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*10*

( Abu Turab an haifeshi a shekara ta alif dubu d'aya da d'ari tara da saba'in da d'aya, shikuma Abdulmajid an haifeshi a alif dubu d'aya da d'ari yara da saba'in, karku manta farkon labarin a shekara 1970 aka fara wanda ya kasance ranar sunan Abdulmajid, a kuma shekarar ne Sarki ya auri Basira har ta samu ciki.)

_Wannan tuni ne_

********
Hisham ya fito sai dai baiga kowa a waje ba, ciki ya koma cikin halin ko in kula dan shi babbar damuwarsa bai wuce ya d'au mataki a kan Basira da d'anta ba dan tuni aka sanar dashi suna raye, ba shakka inya sake wani yunkuri za'a gano bakin zaren shiyasa yake tunanin in suka tafi a hanya ya zama dole ya san yanda zaiyi kafin su karasa garin.

*********

Magajiya tun bayan tafiyar Hisham ta rasa inda zata sa kanta, ya zama dole ta fitoda wata sabuwar hanya ta yanda zatai in har d'an ya dawo, ita ta kasa yarda da komai ma.

Mamaki ne ya kamata jin sallamar Jakadiya, ta dade sosai kafin ta bata izini, Jakadiya ta shigo tare da washe baki, ta matso kusa da Magajiya ta zauna a kasa sannan ta kalleta ta mata jinjina tace " Sai ke Sarauniyar da babu irinta, ba aiba kuma baza'ai irinki ba, kinci dubu sai ceto takawarki lafiya matar sarki, takawarki lafiya mamar sarki, takawarki lafiya Haj......."

Wani banzan kallo Magajiya ta mata tace " me kike aikatawa yanzun?"

Jakadiya ta washe baki tace " wato Ranki ya dade matsala aka samu ai yayatace bataji dadi ba shi......"

Wani mugun murmushi Magajiya ta sakar mata tace "Babu ruwan kwai da aski, abinda nakeso naki shine ke din wacece?"

Yawo ta had'iya sannan tace "taki ce sai dai......"

Magajiya tacigaba " waye ya baki wannan matsayin wanda kike takama dashi?"

Jakadiya tai zuruzuru da ido, da kyar tace " kece."

Magajiya tai wata 'yar bazawarar dariya tace " kinsan da haka ke har kin kai matsayin da zakiyi tunanin yimin karya?ke d'in wacece da har...."

Da sauri Jakadiya ta sa gwiwowinta a kasa tace " Magajita tuba nake, sai dai kafin ki yanke hukunci yakamata ki duba yanda nake miki biyayya, nasani sarai Yarima ba......."

Gaban Magajiya ne ya fad'i ta kalli Jakadiya a tsorace, dama Jakadiya tasan wannan ce kadai hanyar dazaisa ta tsira inhar ta nuna mata ta san sirrinta.

Jakadiya tai saurin rufe bakinta tana waige waige tace "tuba nake ranki ya dade, wannan sirri ne da zan rikeshi har kabari na, tuba nake da subutar baki."

Magajiya ta danyi kifikifi da ido sannan ta daure tace " me kike san cewa?"

Jakadiya tace " tuba nake Ranki ya dade ai sirri ki nawa ne, baza'aji wannan zance daga gareni ba."

Ganin tabbas Jakadiya tasan wani abu sai dai da alama batasan duka ba yasa ta daure tace " tashi kije ni ina bukar hutu."

Nan Jakadiya tai waje da sauri.

Tana fita tai dariyar mugunta tace " ni da gidan nan da matsayina mutu ka raba."

*********

Sarki ya kasa zaune ya kasa tsaye, yau ya kamata su Hisham su dawo sai dai yajisu shiru hakan yasa da kansa yai tattaki zuwa b'angaren Magajiya.

KAINUWA....Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang