Kainuwa....80

7.1K 592 51
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*80*

Kowa da ke cikin gurin ne ya zuboma Hisham ido, jiki a mace ya shigo ya zauna.
Galadima ya kalleshi sheke ke ya tuno abinda dansa ya sanar dashi, ba shakka ko waye ya ji dolene yasan da hannun Hisham a wannan lamarin inba haka ba ta yaya ya san inda aka kai Abdulmajid?
Gyaran murya da sarki yai ne yasa kowa ya nutsu, Takawa ya kalli Hisham sannan ya kalli Alkalin yace " a fara."
Nan alkalin ya ciro takardar ya fara karantawa kamar haka.
" A jiya ranar lahadi ne aka kawo karar Hisham wanda akace ya nemi da a kama Abdulmajid wanda hakan ya jawo masa karaya a kafarsa da kuna manyan ciwuka a gab'obin jikinsa."
Kallan Hisham yai yace " Hisham kana da abin cewa a game da laifin da akace ka aikata?"
Kalaman Abdulmajid ne suka fad'omai ya kalleshi yace " ta yaya zan so wani abu ya samu d'an kanwata? Ni fa na kasa fahimtar takamaimai me na aikata"

Galadima yace " ina muka san manufarka?"
Turab ne ya d'ago sannan ya kalli Hisham ya juya ya kalli Alkali yace " Gaskiya ni kaina na kasa gane takamaimai me ka aikata, zuwa gun d'aurin aurena dakai ka tambayeni a inda na taho? Ko kuwa jin Abdulmajid ya taho a motar daya kamata in taho da kaji hankalinka ya tashi? Ko kuma ganin da Sabi'u yama ka je ka d'auko Abdulmajid? Ni kaina Mai Martaba na Kasa gane mai Waziri ya aikata."

Hisham yace " dan na tambayeka in da ka taho gani nake ai ba laifi bane."
Turab ya jinjina kai yace " haka ne, sai Dai ya akai kasan inda Abdulmajid yake farat d'aya? Ba tare da bincike ba?"
Hisham ya d'ago ya kalli Sarki.
Sarki ya kalleshi yace " amsarka nake san ji."
Hisham ya daure yace " nima ba sani nai ba bincike nai har Allah ya kaini gun."
Galadima yace " gaskiya kam, ai hakan zata iya faruwa, amma ni a sanina Sabi'u baiga alamar bincike a tattare da kai ba."
Hisham ya kalli Galadima cikin takaici sai dai bai amsa ba.
Turab ya mike ya dawo gefen da Hisham ke zaune ya kalli sarki yace "Ranka ya dade menene dalilin daya sa Abdulmajid ya shiga motar da ta kasance mota ce wanda Ango zai shiga?"

Kallan Hisham yai yace " Waziri mai kake tunani?"
Hisham ya kalleshi dan bai fahimcu me yake nufi ba.
Turab yace "baka tunanin yaji wani abu game da abinda zai faru?"
Idanu Hisham ya zaro yace " kanaso kacemin Abdulmajid yasan abinda zai faru a ranar?"
Turab yace " ranar? Wace rana kenan?"
Hisham kallansa yai sannan yace " bansan me kake so kace ba."
Turab yace " zata iya yiwuwa, sai dai da alama bakwa tunanin abinda Abdulmajid yakeji a wannan lokacin, ace yayan mahaifiyarsa shine ya nemi halaka mai rayuwa, ko meye ribarka........"
Cikin zafi Hisham yace " kai yaro, ya isheka haka, har yaushe aka haifeka da zaka zo ka dinga d'aure magana? Hauka nakeyi da zan nemi halaka Abdulmajid? Tsautsayi ne dai ya afka ya shiga motar da bai kamata ya shiga ba, amma ni ban yarda ya ji ba, ni ina tunanin kai ne ka sashi ya shiga motar ma."

Kallan Turab sukai, Shikam bai san sanda ya sa dariya ba, yana dariya ya sunkuyar dakai yace " tuba nake ranka ya dade, bansan sanda dariya ta kwacemin ba, ni? Meye ribata in nayi hakan?"
Hisham yace " ka hau mulki ba tare da matsala ba mana."
Turab yace " kana so kace in har d'aya ya kauda d'an uwansa a tsakaninmu d'ayan zai hau mulki ba tare da matsala ba kenan?"
Hisham yace " Sai ka tambaya?"
Turab yace "ahhh na gane, amma in na kusa damu ne suka neman taimaka mana gun rage mana iri fa?"
Hisham yace " ban fahimceka ba."
Turab ya kalli Alkali yace " ina so a duba maganar Hisham kamar haka, na farko yace Tsautsayi ne dai ya afka ma Abdulmajid ya shiga motar, na biyu zuciyarsa tana tunanin halaka junanmu shine hanyar da ya fi cancanta d'ayan mu ya hau mulki, sannan bai musa ba akan shi da wani sun aikata wani abun tunda sanda na cemai Abdulmajid yaji bai musa ba akan bai san me yaji ba sai cewa dayai wai bai yarda yaji ba."
Ji sukai " Abu Turab kuka so ya shiga motar?"
rq
Gaba d'aya kallan mai martaba sukai wanda idanunsa ke kan Hisham, ya cigaba " motata dana bada ta ango ce, menene dalilin dayasa ba'a tare ko wace mota ba sai ta Ango?"

KAINUWA....Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt