Kainuwa..51

6.6K 479 51
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*51*

Zaune yake a cikin wani had'ad'an gun hutawa, a hankali yana cin inibin dake gabansa sannan yana duba littafin hannunsa, lumshe ido yake yi saboda yanda yakejin dadin rayuwa, cikinsa ne yaji ya murd'a nan fa wani azababben ciwo mai tada hankali ya rutsashi, baisan sanda ya durkuso kasa ba yana murkususu saboda azaba, idannan nasa yayi jaa kamar garwashi, tsananin tashin hankali da rad'adin da ya ke ciki.

Jiyai an sakar masa wata irin dariya na keta da sauri ya d'ago dan ganin wani mugun ne wannan ba taimako sai dariya?

Magajiya ce cikin wani had'ad'an shiga tayi kwalliya sosai, dariya take sosai.

Abdulmajid ne ya fito daga bayanta shima yana dariya harda kyakya tawa.

D'ayan gefen kuma Hisham ne ya fito shima dariya yakeyi sosai, nuna shi suka shiga yi suna dariya.

Basira ya gani a kasansu a kwance wanda baisan ko tana raye ba ko ta mutu.

Sannan Abdulmajid yana rike da igiya yana jan wata yarinya a kasa, kallan yarinyar yai ga mamakinsa sai yaga Mairo.

Kirjinsa ne ya d'au zafi, Khadija ce ta taho da gudu gunsa tana kuka kamar ranta zai fita, da sauri Hisham yasa hannu ya fizgota.
Jiyai gaba d'aya ya kasa numfashi da sauri ya bud'e idanunsa.
Cikin tashin hankali yake kallan d'akin, ga zufa da yai sharkaf.

Zama yai cikin tashin hankali yana addu'oi, ba shakka wannan mafarkin ya tsoratashi, shi yasa baccin yamma bashida kyau.

Mikewa yai ya sauko daga kan gadon, sai dai jiyai kafafunsa na rawa.
Gado ya dafa tare da runtse idanunsa.

Ya dade a haka kafin ya daure ya shiga ban d'aki.

Bayan ya fito ne ya zauna a bakin gado, ba shakka mafarkin ya bayyana karara kamar gaske.

Ga kansa na mai wani azababben ciwo.
Sabi'u ne ya leko yace " Ranka ya dade ka tashi? Wai daga shigowa sai in tadda kai kana bacci?"

Turab ya kalleshi kawai baice komai ba.
Sabi'u yacigaba " dama aiko wa akai in anyi magrib zakaje ku gaisa da Fulani."
"Gobe da sassafe zamu koma gida."
Abinda Sabi'u yaji ya fad'a kenan.
Mamaki ya kama Sabi'u da sauri ya karaso cikin d'akin yace " Mutumina lafiya?"

Turab ya kalleshi, ganin yanda idanunsa sukai ja ya matso da sauri yace " Yarima Lafiya?"

Turab ya mike yazo kusa dashi kawai ya dafa kafad'arsa sannan ya wuce.
Waje ya fito ya tsaya yana kallan sararin samaniya, me yasa yakejinsa haka?

Bayan Magrib jakadiya tazo ta raja Abu Turab gun Fulani, sosai ta karbeshi sannan itama ta rokeshi akan rikon Bilkisu, irin amsar dayaba Mai Martaba ita ya bata.

Haka ya taso cikin gamsuwa da yanda sukesan 'yar tasu.

Munnira ce ta biyoshi da sauri ta mikamau wata takarda.
Amsar takardar yai ya kalleta yace " ta menene?"
Munnira tai dariya tace " UmmaBilkisu ce tace in baka."
Amsa yai yana cewa
" Yau Umman taki rowar ganinta take min?"
Munnira tace " zaka ganta gobe ai."

Bud'e takardar yai yana cewa "Gobe zan tafi da safe."
Kallan mamaki tamai tace " Amma UmmaBilkisu vata sani ba?"
Kai ya d'aga yace " nima dazun na yanke shawarar haka, amma zan dawo ko zuwa sati biyu ne."

KAINUWA....Where stories live. Discover now