Kainuwa....49

6.1K 499 45
                                    

.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*
_Gareku 'Yan Ayusher Fan Club, wannan Shafin naku ne kacokal...Allah ya bar zumunci_

*49*

Sarki ya kalli Abdulmajid sannan ya kara kallan Barde wanda duk jikinsa ya gama mutuwa.
Gyaran murya Sarki yai yace " Zan duba maganarka, sannan bana jin hakan dakai ya kamata, Mahaifinta ya kamata ka sanarmawa sannan nima ka samen ka fad'amin hakan ne zai sa musan abinda ya kamata, bawai dan kana d'ana ba zakai tunanin dole namaka duk abinda kake so."

Abdulmajid yai kasa dakai yace " Tuba nakeyi."

Bayan ya fito, Hisham ya taho shima da sauri.
Tsayar dashi yai ta hanyar kiran sunansa.
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalli Hisham.

Hisham cikin sauri ya karaso yace " Abdulmajid menene hakan? Wace irin Mairo? Wacece ita da har zaka zo cikin fada kace kanaso a baka?"

Abdulmajid ya kalleshi cikin rashin kulawa da abinda ya fad'a yace " wacce nakeso kuma zan aura."

Hisham yace " Abdulmajid yar gidan barde ce fa, me kake tunani?"
Yace " D'an 'yar gidan Barde ce sai me? Ni wai kawu me yasa kai da Umma bakwa duba halin da nake ciki ne? Me yasa bakwa tausayawa soyayyar da nake mata?"

Mamaki ma sam ya hana Hisham magana, Abdulmajid bai jira jin wani abu ba kawai yai gaba.
Yana kokarin shiga b'angarensa, wata baiwa daga b'angaren Magajiya ta karaso da gudu tace "Yarima ana kiranka."

Nan ya juya zuwa b'angaren Magajiya.

A tsaye ya ganta a cikin d'aki yana shiga ya rufe kofa, matsowa tai inda yake ta zuba mai wani mari, jikinsa sai daya amsa, tsoro karara ne ya bayyana a idanunsa dan yanda yaga bacin rai karara a idanunta.

A hankali ya zauna a inda ya fara zama kansa na, juyowa tai cikin tsananin takaici tace "Abdulmajid kai harka isa har ka isa ince karkai abu kayi? In haifeka a cikina kace kana neman kafi karfina? To bari kaji tunda nake a duniya duk wani buri nawa ba wanda ban cikashi ba sai abu d'aya wanda shikad'ai ne nake danasanin gangancin danai, daga shi kuma bana bukatar wani danasani a rayuwata, baka isa kai ka sani bakin ciki ba....."
Katseta yai yace " Umma yanzu menene aibun auren Mairo?"
"Aibu? Shi kake san ji? Idan har ba so kakeyi rayuwarta ta shiga cikin kunci ba kai gaggawar janye maganar nan."

Yace " indai har a kusa dani zatai kuncin nikam banajin zai damen."

Kallansa tai cikin tsananin mamaki tace " Abdulmajid."

Kasa yai da kansa kawai baice komai ba.

Khadija ce tai sallama bata jira ba ta shigo da sauri ciki.
Magajiya ta kalleta, gaban Abdulmajid tazo ta tsuguna tace " yaya yanzun nan Umma ta aikoni in kawo sako naji ana zancen kana san auran Mairo, Yaya Meke faruwa?"

Kansa ya kawar gefe, hawaye ne ya fara zubo mata ta shiga girgiza kai tana cewa " yaya please kabar maganarnan, Mairo itace Ya Turab yake so ta yaya zaku zama kune sanadiyyar kuntata masa rayuwa, na sani ba santa kakeyi ba, in har ni bazan zauna kusa dashi ba dan Allah yaya kabar ta ta zauna gun Ya Turab......."

Kuka ne yaci karfin ta mamaki ne karara ya bayyana a idanun su duka su biyun, Magajiya ta juyo tace " Turab ne yake san wa? Mairo?"

Khadija kuka kawai takeyi tanacewa "Dan Allah yaya ka janye maganarnan."

Abdulmajid ya buga mata wani harara yace " Khadija kina nufin saboda farincikin Turab kinaso ni in kuntata? Farincikinsa ya fiye miki?"

Kallansa tai tana girgiza kai tace " ba haka bane yaya, inka duba rayuwarsa zakaga abin tausayi ne shi, yaushe ya fara gani? Sannan waye gareshi a kusa dashi?"
Jitai an fincikota a tsorace ta d'ago Mahaifinta ta gani, Magajiya na tsaya tana mamakin abinda takeji.

KAINUWA....Where stories live. Discover now