Kainuwa...38

6K 494 45
                                    

.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

_Gaisuwa Gareki Kawar Arziki *Faizah* nagode kwarai da kauna, Allah yabar zumunci Ameen suma Ameen_

*38*


A kwanar gidansu ta tsaya, tana tsaye tana kallan gidansu daga d'an nesa, ita a rayuwarta bataji zata iyama wani saurayi kara, Abu Turab take so ba taji zata iya zance da wani.

Juyawa tai, sai dai ina zata? Idanunta ta d'an runtse kadan sannan ta cije lab'anta, a hankali take takawa harta kusa isa gidan.
A waje taga mahaifinta shida masu musu hidima na gida, sunyu carko carko.

Tsoro yasa tad'an hanzarta dan ta d'auka ko wani abun ne ya faru.
Tana zuwa kusa dagun fitilar dake kofar gidan ta hasko ta.
Wani daga cikinsu yace " Yallabai gatannan."

Nan kowa ya juyo ya kalleta, Waziri ya kalleta cikin takaici sai dai alama ya mata akan ta wuce ciki.
Nan ta shiga gida, ko d'aki bata shiga ba ya shigo ransa a b'ace yace " Khadija ke ba....."
Kallan idanunta yai yaga sunyi jaa sosai da alama har kuka ma tayi.
Yana san yarinyar jiyai bazai iya mata fada ba, yace " jeki kintsa kizo ku gaisa da Saifullahi, tun dazu yake jiranki."
"To, amma banyi sallah ba."

Kiyi sauri kiyi kizo yana jiranki.
Tace to.
Juyawa tai ta shiga d'aki.
Ummanta tana kitchen tana duba kayayyakin abincin da za'a kaimai.

Sallah tai sannan ta gyara fuskarta, ta jawo hijabinta ta zura.
Mahaifiyarta ce ta shigo kallanta tai tace " Khadija ina kika je?"
Shiru tai hakan yasa tace "ki canza kaya kisa sabo."
Tana kainan tai waje.
Labanta ta ciza na takaigi sannan ta kwabe kaya tasa wani.
Fitowa tai ta nufi inda Umma ta nuna mata.

Sallama tai sannan ta shiga.

Saifullahi ya amsa sallamar tare da kurama kofar ido.

Tunda ta shigo yake zuba mata murmushinsa na yaudara har sai dataji kafafunta suna neman hard'ewa.
Zama tai daga can nesa dashi, sannan a hankali ta motsa baki tace " Ina wuni?"
Gani tai ya mike ya dawo gabanta inda take zaune, kanta na kasa sai gani tai ya sunkuyo inda kanta yake cikin salonsa na soyayya yace " Gimbiyata sai yau Allah yai."

D'agowa tai tare da d'an jan jikinta baya tace " Saif meye hakan?"
Ajiyar zuciya yai yace " tun randa na ganki a kano sai yau Allah yai na sake ganinki, nikadai nasan dadin danake ji."
Baki ta tabe ba tace komai ba.
Gani tai ya sake matsowa ta d'ago da sauri tana kallansa tana zazzare ido.
Dariya taga yayi yace " Sry mikewa zanyi so nake in kara ganinki sosai."

Mikewa yai ya koma gefenta kadan ya zauna yace " Khadija dan Allah ki saki jiki dani, sam banasan inga mace tana wannan kunyar."

Kallansa tai tace " Ai kuwa mace da kunya aka santa tayaya za'ace ta daina?"
"Oh God c'mon my Khadija."

Yanda yaga tana kallansa alamar tsananin mamaki yasa ya saki dariya yace " Khadija wannan kalan fa? Gaskiya xanji dadi in mukai aure dan inasan wannan kalan dayawa."

"In mukai aure kamar ya kenan?"
Gani tai ya canza fuska yace " bangane ba, kinaso kice bakisan wani watan iyayena zasuzo gaisuwa ba? Daga nan kuma sai me?"

Tsananin mamaki da fargabar kalamansa ne yasata yin shiru, nan fa ta tuno da abin begenta Turab.
Jitai idanunta sun ciciko.
Saif ya kalleta yace " Deejah na menene?"

Kaina ke ciwo, tun d'azu.
Ya kalleta kalar tausaya yace " sannu."
Mikewa tai tace "Saif i am sry amma dan Allah zan je na kwanta, kaina saramin yakeyi."

Kai ya jinjina yace " sannu, jeki kwanta nima gidan kawuna zani gobe da safe zan wuce kano."

Tace " Nagode Allah ya kiyaye hanya."

Tana kai nan tai waje.
Shiru yai sannan ya mike tare da murmusawa.

Tana fita tai hanyar d'akinta jitai Ummanta tace " Khadija? Ya tafi ne?"
"Eh."
Ta wuce ciki.
Kwanciya tai ta shiga yin juyi akan gado.

**********

Magajiya zaune ta a lissafi da hannunta wanda nikaina bansan me take lissafawa ba, Abdulmajid ne ya shigo rai a b'ace, yana shiga ya zauna dabas.
Harararsa tai tace " kai kuma meye hakan? Zaka shigo ba wani tafiyar takama da isa irin na magajin Sarki?"

Kallanta yai yace " Umma ki taimaken ki auramin Mairo, in ban koyama yarinyar nan hankali ba ta hanyar auranta ba, banaji hankalina zai kwanta."

Wani mugun kallo ta bugamai tace " in har koya mata hankalin kake san yi da gaske ai basai ka aureta ba, kawai ka sa a hukuntata."

Kai yad'an sosa yace " Ai Umma.."

Katseshi tai cikin fada tace " badai auren Mairo bakam, nasan sarai me kake nufi, kai maza ka cireta a ranka, na fadama
"

Mikewa yai cikin takaici yai waje....

Ita kuwa Mairo yau bakin ciki duk ya hanata sukuni gashi ta ma Abu Turab girki da kanta, haushi da takaici duk ya gama isarta tana kallo kishiyar babarta da 'ya'yanta suka cinye abincin.

***********

Washegari an rufe idan Abu Turab, mutane sai zuwa dubashi akeyi kowa na kawo abubuwa na kayan dubiya.

Bayan azahar yana zaune yad'an samu ya zare abin da aka d'aure idanun nasa dan hutawa, Garzali ya shigo yace "Ranka ya dade Mairo ce."

Bai maida ba yace "ta shigo."

Shigowa tai fuskarta d'auke da murmushi.
Ta karasa kusa dashi inda kujera take ta zauna, sannan ta kalleshi tace " Inna wuni yaya."
Bai amsa ba yace " Hajiya Maryam na d'auka jiya zan ganki?"
Baki tad'an turo tace " wani bunsuru ne ya tare mana kofar gida ya hana ni fita."
Bunsuru?
Tace eh, amma karka damu ya gaji ya tafi.

Yace " ce miki nai na damu?"
Fuska ta d'an tsuke kad'an tad'an juya kai tace "ba kara?"

Cikin rashin zato taji yace " meye tsakaninki da Abdulmajid?"

Kallansa tai cikin mamaki, zatai magana sukaji an bud'e kofar da karfi.

Abdulmajid ne, Garzali na bayansa yana kokarin mai magana akan karya bud'e.
Abu Turab ya kalleshi sannan ya kalli Garzali yamai alama daya koma.

Abdulmajid me ya karaso ransa a b'ace ya kalli Mairo sannan ya kalli Abu Turab yace " Tsakaninmu kake tambay?"
Abu Turab yamai wani kallo sannan yace " banaji dai acikin kalamaina na sako ka,sannan bakasan laifi bane shigowa mutum guri ba tare da neman izini ba?"

Abdulmajid ya matso saitin Mairo ya tsaya yace " ke harkin isa jiya inzauna jiranki amma kiki fitowa? Shine yau dan kin rainamin hankali in ganki anan?"

Abu Turab a ransa yace " Au kaine Bunsurun?"
Baisan sanda yai dariya ba.
Hakan ya kular da Abdulmajid matuka.
A zuciye ya kalleshi yace " kai kuma me kakema dariya?"
Abu Turab yace " wani bunsuru na tuna, sannan inka gama abinda kake plz kai waje dan na tabbata ba dubani kazo ba."
Kallan Mairo yai yace " wuce muje."
Harararsa tai tace " inje ina? "
Wuce muje nace ko?
Tace " yau naga ikon Allah a matsayinka na wa?"
"Mene?"
Tace " ban fahimta bane ina zaune kawai kace in tashi muje."
Ransa yakai kololuwar baci dn dama Magajiya ce tasashi wannan zuwa dubiyar anma da yasan abinda zaigani kenan ko abinda zata mai kenan a gaban yaran nan da baizo ba...
Kwafa yai sannan yai waje a zuciye.
Yana fita taja tsaki.



*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*

KAINUWA....Where stories live. Discover now