Kainuwa...28

5.7K 429 5
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*28*

B'angaren Mahaifiyarsa ya nufa, tana zaune gefenta kuma Lantana ce, daga bayanta kuma a tsaye Mairo ce take mata kitso, jiki a sanyaye yai sallama.
Dukansu suka amsa nan ya karasa ya zauna a kasa tare da lankwashe kafafunsa.
Basira ta kalleshi sai dai batace komai ba, d'agowa yai yace " Umma gobe zani Kano."
Gabanta ne ya fadi dan kuwa tasan me zaije yi kanon.
Sam ta manta da Mairo dan kuwa hankalinta ya tashi, ta kalleshi tace " ka amince da ganin yarinyar ne ko kuwa har auren?"

Idanu Mairo ta zaro cikin tsananin tashin hankali, kallan Abu Turab kawai tayi, shima jin kalaman Basira yasa ya d'ago ya kalli Mairo.
Ganin yanda idanunta sukai yasa ya kalli Basira kansa na kasa yace "Mairo bamu guri."

Jin haka yasa Basira ta juyo da sauri ta kalleta, ganin yanda kwallq ta ciciko mata yasa tace " Lantana shiga da ita d'aki
"
Mikewa Lantana tai ta ja ta ciki, suna shiga ta zube a kasa tare da hade kanta da gwiwarta, ba kuka take ba sai dai yanda takeji a ranta tabbas taso ace ma kukan takeyi.

Tana iya jiyo muryar Basira sama sama tana cewa " Abu Turab nifa wannan hadin auren bai kwantamin ba, nafisan ka auri Mairo ko dan samun nutsuwarka da kuma kwanciyar hankalinka."
Dan murmusawa yai yace " Umma kinaso ne na karya umarnin Sarki ko me? Abba ya kiranine a matsayin Sarki bawai a matsayin Uba ba, sannan maganar Mairo nicewa tai tana sona ko kuwa nice nace ina santa?"
Shikam yasan tana sansa sai dai yayi hakan ne dan sa Umma ta saduda, ya cigaba da cewa " itama ta kanon xan dai jene kawai inbi Umarnin da aka bani amma tana 'yar sarki guda d'aya tilo mai zatai dani? Makaho?"
Basira cikin bacin rai tace " Da farko amsarka xan ba, na tabbata kai kanka kasan Mairo tana sanka, sannan kaima nasan haka, sannan na biyu shi mai martaba cewa yai kaje a Makaho?"

Gaban Mairo ne ya fadi, Lantana jin haka ta taso fa sauri daga inda take a d'akin tace " tashi ki shiga can ciki."
Mairo ta kalleta tama kasa magana mikewa tai a hankali ganin yanda ta tsaya kamar me shirin faduwa yasa Lantana ta riketa, ji sukai Abu Turab yace " yace inje a duk yanda naso, nima haryanzu ban tantance a me zanje mata ba."
Jitai kanta yayi wani irin sarawa, cikin rawar murya ta kalli Lantana tace " meke faruwa?"

Lantana ta kamata suka fara tafiya, sai data kaita canciki sannan ta kalleta tace " ba abinda ya faru nikaina bansan me suke nufi ba."

Mairo ta kalleta tace " amma dai ba kina nufin in yarda da kalamanki ba ko?"
A makaho xakaje mata? Ta maimaita maganar da Basira tai sannan tacigaba da cewa " me hakan yake nufi? Duk wanda qwaqwalwarsa take aiki na tabbata xai gane magana ce aka yita mai ma'ana biyu, a makaho zakaje mata?ko da ido?"
Lantana ta kalleta cikin tsoro, Mairo ta mike ta tsaya gaban Lantana tace " zan gyara tambayar dana miki d'azu, Yaya yana gani?"

Idanu Lantana ta runtse batace komai ba, Mairo tace " zan kara gyara tambaya ta, Lantana meyasa yake pretending din baya gani?"

Lantana ta girgiza kai tace " nima bansan komai ba, da sauri tabar d'akin tare da janyo kofa."

Mairo tai shiru tana tunani, me yasa yaya yana gani yake nuna baya gani? Wani irin abu ne yau takeji haka? Abubuwan da sukai ta faruwa dashi yana yari ta tuna, kai ta girgiza tace bazai yiwu ace pretending yakeyi tun da ba sai dai in warkewa yai."

A can bangarensu Basira kuwa, kallansa tai tace " Abu Turab harga Allah zaka cemin baka san Mairo tana sanka ba?"
Kallanta yai yace " Umma!"
Tace " ni mahaifiyarka ce nasan abinda zai taimakeka gun samun farincikinka, Mairo zata kula dakai, zata taimakeka ni aguna ita kadaice zata dawoma da farincikinka."

Idanu ya runste yace " nifa Mairo kanwa tace ban taba tunanin zaman aure da ita ba."
Jiyai tace " sai ka fara yanzu."
Mamaki ne ya kamashi yace " Umma nawa nake? Shekarata kwatakwata nawa? Taya zakumin zancen auren mata ba d'aya ba har biyu a rana d'aya wanda kuma duk cikinsu ba alakar soyayya dake tsakaninmu?"
Basira tace " Ba takura maka zanyi ba sai dai inaso ka duba ra'ayina ka kuma ba shawarata lokaci mai yawa."
Sunyi shiru kafin tace " tashi kaje."

Mikewa yai ya fita, d'akinsa ya shiga ya kwanta akan gado yana kallan sama.

Mairo ce ta fito kana ganinta kasan tana cikin wani yanayi, Basira ta kalleta tace " Mairo jeki gida zansa a karasa min kitson."
Kai ta girgiza alamar a'a tace " a'a Umma bari na karasa miki."
Basira tace " jike Mairo, ninace kije ai."
Jakarta kawai ta d'auka ta mata sallama tai waje.
Tafiya kawai takeyi amma zuciyarta fal take da tunani kala kala tama rasa ta inda zata samo amsoshin tambayoyin.

Jitai an fizgo hannunta, a tsorace ta juyo, janta kawai taga yayi soron kusa da gun ya sata a ciki.
Hannunta ta shiga fizgewa ta hada cewa " Malam meye hakan? Sakarmin hannu ko?"
Baisake ta ba ya d'ora da cewa " da dan rashin mutunci kina ganina kika wuce ni?"
Kallansa tai cikin takaici tace " Malam sakeni dan Allah, ni ba muharamarka ba zaka wani dinga rikeni? In magana zakamin kamin da baki."
Murmushi taga ya saki yace " Karki damu saura kiris ki zama matata dan na kula shi kadai ne yanya mafi sauki da zan daidaita miki sahu."

Kallansa tai cikin takaici tace " in zama matarka? To ko nidin baiwa ce banaji kamada damar yanke hukunci akaina bare kuma....."
Katseta yai tare da sakin hannunta yace " kin dai san nidin waye kin kuma san matsayina a garin nan, ko Mahaifinki bai isa in yanke hukunci ya canza min ba."
Dan karamin tsaki taja sannan ta kalleshi ido cikin ido tace " Abdulmajid kake ko wa?"

Idanu ya zaro ya kafeta dasu, tacigaba " Zan maka kashaidi xa gargadi na farko kuma na karshe, in har zamuyi magana dakai ka kiyayi min abubuwa guda biyu, na farko kada ka kuskura ka kara rikeni ko ka taba ni ko da kuwa hijab din jikina ne, na biyu kuma kada ka kuskura ka dinga sako iyayena in muna magana, ni yanzu banda lokacin ka abinda ke gabana yafi karfin na tsaya ina bata lokacina."
Matsawa tai da nufin wucewa, fizgota yai da karfi ya bugata jikin bango yace " ke harkin isa ina magana kina magana, har kina da matsayin da zaki kira sunana gatse gatse har kice zakimin gargadi?"
Ajiyar zuciya tai tace " in kaji haushi inji sammaci."
Tana gama fadar haka ta ture hannunsa tai waje.
Kallan bayanta yai cikin kuluwa yace " mu zuba mu gani, ina tausaya miki in kika shigo hannuna, auranki kuma ya zama dole a gareni."
Yanajin haushin yanda baya iya yanke mata hukunci duk wulakanci da zatamai.

Itakam ranta a bace tai gaba, tana kokarin fita taga wata kamar Khadija ta wuce, binta tai da kallo cikin mamaki da san tabbatar da abinda zuciyarta ke zargi.

Khadija kam bata kula da ita ba dan ba lafiya ce ta isheta ba yanzun ma daliline ya shigo da ita.


*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*

KAINUWA....Where stories live. Discover now