Kainuwa..48

6.4K 494 28
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*48*

Mairo ta dade a tsaye kafin tai waje cikin tsananin b'acin rai.
A tsaye ta ganshi yana tsaye ya juya baya a jikin motarsa, hannunsa sanye cikin aljihun rigarsa.
Tama rasa dame zata karasa mai.
Tsayawa tai kawai tana tunanin wacce kalma ce mai tsananin muni da ya kamata ta fad'amai?"

Juyowa yai dan jikinsa ya bashi ana kallansa, a hankali ya tako har inda take, tana tsaye kawai tana kallanshi.
Yana zuwa inda take yace " Amince Agareki Matar Abdulmajid ko ince Gimbiya Maryam wacce zata gaji Magajiya."

Wani kallo kawai tamai dan ta ma kasa magana, murmushi yai sannan ya d'an kara matsowa yace " Kin rasa bakin magana ko? Na tabbata dama zaki fahimceni, zaki kuma amince da soyayyata."

Kallansa tai cikin takaici sai kawai ta tsartar da yawo ta gefensa ta juya zatai ciki.

Ransa yakai kololuwa gun baci da sauri ya sha gabanta yace " me kike nufi da abinda kikai? Kyama ta kike?"
Fuskarta a had'e tace "Kyamar hallayanka nake, ta yaya zakazo ka samu mahaifina bayan kasan ba sanka nake ba? Ko kana tunanin hakan dakai shine zaisa a auramin kai?"

Lab'ansa ya d'an ciza yace "me kika d'auken? Kina tunanin sanar ma mahaifinki danai nayi ne dan in aureki?"
Mairo tamai kallan ba haka bane? Gira ya d'aga mata ya na kad'a yatsunsa yace " kin makaro Mairo dan kuwa bazaki taba jin shirina a kan aurenki ba, sai dai na d'au alkawari a zuwa daren yau zakisan matsayina a garin nan zakuma kisan nid'in yaro ne ga Sarki Abdussamad."

Yana kaiwa nan ya juya ya shiga mota yai gaba.
Da harara ta bishi tace " ba zuwa dare ba inji an shafa fatiha a nan da awa d'aya." Tai ciki.

************

Sabi'e ne ya mike daga kan kujerar daya kwanta ya kalli Sabi'u yace " Me kake tunanin Mai Martaba zai tambayeka?"
Abu Turab dake rike da littafin Riyadul Salihin yana dubawa yace " ina na sani? Sannan meye naka na damuwa da abinda bai shafeka ba?"
Sabi'u ya d'an yi ajiyar zuciya yace "yau ma tafiya zakai kenan ka barni anan ni kadai? Da alama dai ba amfani a rakiyar nan dana maka."

Tsaki yai yace " Kai dai wlh akwai sanjin gulma ni na shiga ciki."
Ya mike ya shiga d'aki, Sabi'u ya shafa kansa yace " ahhh Sabi'u ka zama d'an d'aki, ni ba mace ba."

Abu Turab kam yana shiga ya kwanta yana tunani.
Ta yaya zai warware matsala da kuma hukunta wad'anda suka wulakanta mahaifiyarsa? Suka kuma halaka masa kawunsa? Ina ma bai tab'a sanin Khadija ba a rayuwarsa, ina ma itama muguwace irin iyayenta? Hakan shine zaisa yaji dadin hukuntasu, idanunsa ya runtse da karfi, baisan meyasa ba bayasan Khadija taga wulakantar iyayenta, kuma ya zamana shine silar wulakantarsu wanda takeso tun tana karama.
A da auran Bilkisu zaiyi ne saboda ya kuntatawa Magajiya da kuma umarni na sarki, sai dai a yanzu ya cire wannan a ransa zai auri Bilkisu ne saboda rad'in kansa, tunda wacce yakeso bazai taba samu ba to gwara ma ya aminta da wacce ta fahimceshi wacce kuma ya yarda da ita, Mairo fa?
Idanunsa ya bud'e daya tuno da ita, wata zazzafar iska ya furzar tabbas dama shi yasan a rayuwarsa ba auran soyayya ba kuma farinciki mai d'orewa ya yanke wannan hukuncin ne tun a sanda Mahaifiyarsa ta sanar dashi komai.

Wajen Azahar yai kwalliya sosai dan babbar riga ma ya saka ya saka hula akan sumarsa, yayi kyau sosai da sosai ya saka takalminsa irin mai lankwasan nan na sarauta.

A falo ya tada Sabi'u yanata baccinsa, fita yai.
A waje yaga dogarawa guda biyu a tsaye da alama sun d'an dade suna jiransa.

Suna ganinsa suka matso suka gaidashi.
Yace " tun yaushe kuke nan?"
D'ayan yai kasa dakai yace " tun d'azu muka zo, Mai Martaba ne yace mu tsaya a waje mu jira har sai ka fito karmu takura maka."
Kai ya jinjina kawai yace " muje."

KAINUWA....Where stories live. Discover now