Kainuwa......44

5.9K 461 54
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*44*

Mikewa Magajiya tai daga kan gado cikin tsananin takaicin abinda Turab ya mata, abin haushi jitai baiwarta tana sanar da ita isowar baki dan tayata murnar warkewarta.

Haka ta bada umarni suka shigo, kan gado ta koma ta zauna, kowa yazo tayata murna sai ya jinjinama Turab da kokarinsa wannan abu yafi kular da ita, wasu dan gulma ma so suke suji me ya had'a Abu Turab da Abdulmajid.

In taji haka sai dai kawai tace " zancen mutane ne kawai amma su ba abinda ya had'a su."

Sai wajen Magrib ta samu sauki tai wanka ta sa kaya sannan ta aika a kira mata Hisham.

*******

Mairo kuwa bayan ta ba Umma magani nan ta dafa mata abinci ta bata taci, suna zaune labarin abinda ya faru ya isomusu, wannan labari yasa Umma dan jin dama dama.
Mairo kuwa jitai Abu Turab ya kara birgeta, ba shakka jinin sarauta ma yawo a jikinsa, ba shakka kwakwalwarsa da basirarsa tana aiki.

Sai wajen Magrib ta baro bangaren, Basira nata mata godiya, tana tafe tana murmushi dan ba shakka hankalinta ya kwanta da abinda ya faru.

Sam bata kula da shi ba tadai san ta wuce wasu daga gefenta sai dai bata san su waye ba.
Tana tafiya kawai taji an cafko hannunta ta baya.
A tsorace ta juyo, dan sai da gabanta ya fadi lokacin daya rikota.

Kallan mamaki da takaici ta sakar masa, sannan ta kalli hannunta tace " Malam sakeni ko"
Yace " ina san magana dake."
Tace " To dan kanasan magana dani sai akace ka rike min hannu? Sakeni tun kafin mutane su gamu."

Ga mamakita gani tai ya kara kankame hannunta yace " kina tsoron aganmu ne?"

Kokarin kwace hannunta ta shiga yi tana cewa " meye hakan?"

Abdulmajid ya matso daf da ita kamar zai rungumeta tsoro yasa tai baya, karfi yasa ya rikota, cikin murya mai kama da rad'a yace " zaki biyoni ko sai na rungumeki anan?"

Idanu ta zaro ta cigaba da kokarin kwace hannunta.
Murmushi ya sakar mata yace " Gimbiyata muje ko?"
Ya karasa maganar tare da sakar mata hannu sannan ya nuna mata hanya.

Harara ta makamai sannan tai hanyar daya nuna mata.
Bangarensa ta nufa da ita a tsakar gida taja ta tsaya tare da hard'e hannayenta.
Kallanta yai yace " muje mana."
Tace " muje ina kenan?"
Da kai ya mata alama da ciki.
Harara ta kara makamai tace " d'ad'in abin ni d'in da hankalina bawai a bola ka ganni ina tsince tsince ba."

Dariya yai sannan yama masu kula dashi alama da su fita.
Suna fita ya fara matsowa inda take, hannu ta d'agamai tace " dakata daga nan Malam ko kuma wlh insama ihu."

Yace " Wayyo da naji dadi, ni ai so nake kisamin ma ihun kinga duk abinda za'ayi na riga na mallakeki kenan dan Sarki zai sani auranki saboda rufin asirin mahaifinki."

Kallansa tai kallan tsana tace " wai dan Allah in tambayeka? Ana so dole ne?" Sai kuma ta girgiza kai tace " bama haka ya kamata ince ba, dan ba so na kake ba."

Yace " Mairo abinda zakice kenan? Wlh tunda nake a duniya kece mace ta farko da zuciyata take so, inaji a raina in har ban aureki ba to tabbas zan shiga wani hali."
Baki ta tabe tace " da alama bada gidan sarauta ka dace ba da d'an siyasa ka dace, to ni ko soyayyar ce nace banayi, ko anayi dole?"

Kallanta yai sai dai yanzu fuskarsa ta nuna alamun jin haushin kalamanta.
Mairo tacigaba " Akwai wanda nake so, banaji akwai wani karin bayani dakake nema daga bakina."
Tana fad'ar haka ta juya zata fita.
Da karfi ya jawo hijab dinta, jikin bango ya sata, idanunta ne suka firfito. ya kalleta ransa a bace yace " badai wanda kike so d'in a gidan nan yake ba?"

Kai ta juyamai bata bashi amsa ba, cikin takaici ya kara cewa " badai wanda kike so sunansa Abu Turab ba?"

Juyowa tai ta kalleshi tace " koma wanene wanda nake so d'in banaji yazama dole na sanar dakai."

Hannu yakai kamar zai kifa mata mari dan har ta rintse idanunta, sai kuma taji shiru, a hankali ta bud'e idanunta.
Kallansa tai, hannunsa ya ajiye sannan yace "Mairo ko duk duniya zasu had'u dan ganin ban aureki ba wlh sai dai kowa yayi ya gaji, amma wlh nine mijinki, inkuma harni Abdulmajid ban aureki ba to wlh duk duniya ba namijin daya isa auranki sai dai in bana dorar kasa."

Kafin ta nemo amsar da zata bashi gani tai yayi ciki.
Da kallo ta bishi tama rasa me zatace.
Haka ta fito jiki a sanyaye.

Jakadiya wacce tazo wucewa dan ta dawo daga duba magajiya ta hango Mairo ta fito daga bangaren Abdulmajid, kai ta gyad'a tace " abin harya kai haka?" Dan dama an sha kawo mata gulmar an gansu.

************

Hisham zaune a kilisar Magajiya shi kadai, sai dai kana ganinsa kasan tunani yakeyi.
Magajiya ce ta shigo cikin takunta.
Ta karaso ta zauna sannan ta kalleshi tace " Yaya na d'auka na sanar dakai umarnin mikewa in har zam shigo guri ko?"

Kallanta yai yace " tuba nake Magajiya hankalina ne ya tafi."
Girarta ta d'aga sama tace " a kiyaye."

A ransa yace " ki jira hawan Abdulmajid mulki, lokacin ne zan kiyaye."

Kallansa tai tace " Abu Turab ya wargaza mana shirinmu na hukunta uwarsa."

Hisham yace " ni kaina abinnan ya kona mun rai."
Murmushi tai tace " Abu Turab! Abu Turab! Lalai na yadda jinin Abdussamad na yawo a jininsa, dole ne in zamuyi shiri na gaba sai mun shirya yanda ya kamata."

Kallanta yai sannan yace " ni Magajiya ina ganin kawai mu mikashi kabarinsa."

Wani kallo ta bugamai tace " na d'auka na fadama ba kisa ko?"
Yace " haka kikeso to muyi ta yin shiri yana wargaza mana?har sai yaushene zamu d'aura Abdulmajid akan mulki? Sai mun tsufa? Ko......"
Tsawa ta daka mai tace " YAYA!

Kallanta yai tare da yin shiru, tace " kana tunanin ni Magajiya? Ni Gimbiya Magajiya wacce mulki da takama da isa suka bi jinina, kanaso kace ni wannan Magajiyar har wani yaro wanda na girmi uwarsa, wanda aka haifa kwanan nan zaici galaba akaina?"

Kasa yai dakai yace " Tuba nake ranki ya dade, ni din wa? Ina na isa ince haka? Kawai dai gani nai mutuwarsa tafi sauki."

Idanu ta juya tace" to nace banda kisa, sannan ina tunanin ya kamata Saifullahi ya kawo kudin gaisuwa, in har bamu isa raba Turab da Bilkisu ba dolene mu nemi wanda yakeda mukami a gomnati saboda kudi dan neman taimako nan gaba
"

Hisham yace " to Ranki ya dade angama."

Mikewa yai ya fito, yana fita yabi d'akin da harara yace " wlh zakisan ni kikema tsawa, duk 'ya'yan da kike takama dasu na waye? Daga khadijan har Abdulmajid d'in?

Kiyi ki gama wlh sai nima na gasa miki aya a hannu, wa kike dashi? Wa kike dashi da zai taimakeki? Harni zaki dingama tsawa? Harni zaki ce in mike dan zaki shigo?"
Kwafa yai sannan yai gaba.


**************

Magana ta lafa a gidan Sarauta, yau take juma'a yau kuma Abu Turab ya shirya shida Sabi'u dan zuwa garin na Kano.

Mai Martaba yasa ankawo kaya sosai wanda zasu kai gidan.


*TEAM ABU TURAB 🤝🏻*

KAINUWA....Where stories live. Discover now