Kainuwa.......13

6.1K 478 27
                                    

ẞ 🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*13*

Haka Baffa da Abu Turab suke wuni karatu da addu'oi kala kala sannan daga dare yashiga kashi uku Baffa yake tashinsa su shiga saloli da addu'oi, ko waje baya fita, a kwanansu na hud'u Abu Turab ya fara wasu mafarkai cikin dare yake farkawa wani sa'in da kuka sai dai daga ya tashi yake manta mafarkin.

Sun dage sosai da addu'oi, karatun qur'ani da saloli.

Yau satinsu d'aya kenan Abu Turab na kwance yana bacci hankalinsa a kwance, yau baccib dadi yake masa gashi ko mafarki baiyi ba, Baffa ya sa hannu ya tabashi yace "D'ana tashi lokaci yayi."

Mamaki abin yaba Baffa ganin bai tashi ba, kallan fuskarsa yai sai dai kana kallansa zakasan yana cikin kwanciyar hankali, Baffa yai murmushi sannan yai bismillah ya kara taba shi, addu'ar tashi daga bacci ya fara karantowa bayan ya gama ne ya bud'e ido a hankali duk da yasan duhu kawai zai gani sai dai me? Dishi dishi ya fara gani, cikin tsananin mamaki yace " Baffa ido na."

Baffa ya dafashi yace " menene? Me idan naka yai?"

Murza idan ya shiga yi, Baffa ya shiga karanto addu'oi yana tofa mai, Abu Turab ma yanayi.

Cikin tsananin mamaki da al'ajabi Abu Turab yaga tsohon dake kusa dashi, a hankali yakai hannu inda Baffa yake yace "Baffa!"
Kallansa Baffa yai shima ya kasa magana sai addu'a yakeyi Allah ya taimakesu.

Abu Turab ya tsugunna kusa dashi ya rungumeshi sai ya saka kuka.

Baffa ma hawaye ne ya zubomai dan ya fahimci ya ganshi.

Abu Turab cikin kuka yace " Baffa na ganka, Ina ganin komai ga katifarka, ga kayanka nan a lank'aye, ga kwanan abinci nan ga leda nan a tsakar d'akin, Baffa ina ganin komai."

Idanu Baffa ya lumshe yace " Alhamdulila lalai babu abin bautawa da gaskiya sai Allah."

Tashi muyi alwala muyima Allah sujjada.

Mikewa yai cikin wani jin dadi mara misaltuwa yai waje.

Bayan sunyi addu'ar godiya ga mahallici ne ya kalli tsohon yace " inje gun Ummana?"

Baffa yace " ka barta ta samu bacci zuwa asuba."

Nan ya zauna cikin zakuwa, sai kallan abubuwa yakeyi......

Ana asuba yai b'angaren da gudu jin kofar a bud'e ya shiga bugawa, Basira ta mike a d'an tsorace ta matso tace "waye?"

Cikin jin dadi Abu Turab yace " nine Umma."

Mamaki ne ya kamata da sauri ta bud'e, ya matso da gudu ya rungumeta yana kuka yace " yau Allah yayi na ganki."

Idanunta ne suka ciciko da kwalla, ya saketa sannan ya kura mata Ido yace " Umma na ganki, Umma naganki."

Rungumeshi tai itama tace Alhamdulila.

***********

Satinsa d'aya da warkewa Baffa ya kara kiranta ya mata maganar tafiya nan, tace nan zuwa kwana uku zasu tafi.

Zaune take a d'aki tana kan gado Lantana na kasa haka shima D'an nata.

Kallansu tai tace "inaso duk ku bani hankalinku, akwai abinda nakesan sanar daku masu mahimmanci guda biyu."

Tai d'an ajiyar zuciya sannan tacigaba" na farko zuwa jibi zamu tafi Zariya."

Da sauri Lantana ta kalleta shikam baisan me hakan yake nufi ba shiyasa bai wani damu ba.

Tacigaba " abu na biyu wanda yafi komai mahimmanci shine inaso Lantana kada ki kuskura ko da wasa ki nuna Abu Turab na gani."

Cikin mamaki ta kalleta, Basira tace "wannan umarni ne ba shawara ba."

Da sauru Lantana tace " angama Ranki ya dade."

Basira ta kalli Lantana tace " d'an bamu guri."

Da sauri tai waje.

Basira ta kalli d'anta ta mikamai hannu hakan yasa ya mike tare da zuwa inda take.

Basira ta zaunar dashi kusa da ita sannan ta rike hannayensa biyu tace " nagode kwarai da baka tab'a tambayata mahaifinka ba."

Kallanta yai sannan yai murmushi, ta cigaba " ka nutsu sosai da abinda zance maka."

Kai ya d'aga alamar to sannan ya kada nutsuwa, tace " zamu koma gidan da mahaifinka yake wato gidanku sai dai ina tsananin tausaya maka, da farko inaso kada ka nunama kowa kana gani, hatta mahaifinka ka zama makaho a gaban kowa, ka zama mai ido agabana kad'ai."

Cikin mamaki yace " me....."

Kallan datai mai yasa yai shiru, tacigaba " banaso ka tambayeni dalilin hakan dan kuwa inka mallaki hankalin kanka na tabbata dakanka zaka sanar dani komai, domin zaka samu cikaken amsar tambayarka."

Kai ya d'aga alamar to,tace " Abu Turab!"

Yanda ta kira sunansa da kakkausan murya yasa ya kalleta jiki a sanyaye, tace "kamin alkawarin zakai wannan abin?nasan kasan me alkawari yake nufi a muslunci ka kuma san hukuncin wanda ya karya."

A hankali yace "na miki alkawari ko mai zai saman bazan nuna ina gani ba."

Ajiyar zuciya tai na jin dadin baiwar da Allah ya mata wato na azurtata da wannan yaron, tacigaba " gidanku ba kamar gidajan daka sani bane, dolene ka nutsu kaji me zance, da farko duk yanda ranka yaso da b'acci banaso ka nuna, sannan abu na biyu banaso ka zama ragon yaro."

Kallanta yai baice komai ba, ta riga tasan wannan sai dai ya zama tuni amma tun yana karami ta horar dashi akan haka, ita dama matsalarta shine taurin kansa dan inbaiyi niyyar abu ba ko za'amai dukan dazai kasa tashi tofa bazaiyi ba, wannan hali nasa shi take jiye masa.

Ta riga ta d'au alwashin sadaukar da komai nata dan ta kare d'anta.

Sun dade rike da hannu juna tana mai fada a karshe tace " in muka koma gun Mahaifinka banaso ka yawaita cewa komai sai ni, dolene ka rage nuna damuwarka akaina, kallan mamaki ya mata a ranta tace (in aka fahimci nice komai naka to lalai za'a nemi yin amfani dakai da sunana wanda nikuma ba lalai in iya kwatarka ba daga hannun makirai."

Abu Turab zaune kusa da Baffa yana jin nasiharsa sun dade suna hira kafin Shehu yazo su zauna, Abu Turab yanajin hirar tasu har bacci ya d'aukeshi.

Sukam sunyi hira sosai, da shehu ya mike zai tafi sai yasa hannu zai d'auki Abu Turab akan kaishi b'angarensu.

Baffa yace " barshi anan so nake na kwana dashi."

Nan Shehu ya ajiye shi ya tafi, Baffa ya d'auko rubutun daya wanke ya tashi abu turab yace ya wanke fuskarsa har zuwa kansa, yana magagin bacci ya wanke sannan ya kwanta, Baffa ya dinga mai addu'a sannan ya kwanta.

Jin kiran Sallah yasa Abu Turab ya mike, mamaki ne ya kamashi ganin Baffa a kwance yana bacci, kusa dashi ya matsa ya shiga tashinsa, hankalinsa ya tashi ganin ko motsi bayayi.

Da gudu yau cikin gida b'angaren Shehu, a waje ya sameshi yana alwala matarsa na tsaye kusa dashi.

Abu Turab ya kalli Shehu yace " Kawu kazo Baffa yaki tashi daga bacci."

Inalilahi wa ina ilaihi Raji'un wannan kalma ita Shehu yai ta ambata, dan ko ba'a fada ba ko bai gani ba yasan me hakan yake nufi.....

Allah ya jikan Baffa da Rahama Ameen........

*********

A ranar da akai uku su kuma suka shirya tafiyar tasu.

_Wannan kenan_


*ABU TURAB TEAM🤝🏼*

KAINUWA....Where stories live. Discover now