Kainuwa....27

7.1K 481 40
                                    

.🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*27*

Garzali ne ya biyoshi suka nufi fada dan yanzu aka aiko akan yaje saboda Abdulmajid zai sanar da binciken dayai.
Bayan sun zauna ne Abdulmajid ya dawo tsakiya sannan yace " Ranka ya dade na gama bincike."
Galadima ne yace " to munajinka."
Abdulmajid yai d'an gyaran murya sannan yace " bincike ya nuna mana cewa ba kowa bane ya jawo wannan abin ba sai mahaifiyarsa."

Jin wannan zance yasa mutane suka fara kananan magan magan, Abu Turab kam wani murmushi ya saki kansa na kasa a ransa yace " they take the bait."

Kallan Abdulmajid kowa yai, Mai Martaba ya kalleshi yace " meye hujjarka na fadar haka?"
Abdulmajid ya gyara zama yace " Mahaifiyarsa tanasan asan shi wanene, ma'ana asan shidin d'an sarki ne, sannan tayi hakan ne dan mutane su farga susan akwai wani magajin sarkin bayan ni."

Mai Martaba yace " wannan ita kadai ce hujjarka?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace " tayi abu kala biyu, na farko in har yasa mutane zasu sanshi saboda kayansa da kuma yanayin dokinsa, na biyu kuma ba wanda zaiyi zarginta sai dai kowa yai zargin Magajiya, kunga ta jefi tsintsu biyu da dutse d'aya."

AbuTurab ya d'ago kai yace " Bravo! Ba shakka wannan ma abin dubawa ne."
Mamaki hakan yaba Abdulmajid ya dauka abin zai tadamai hankali.
Barde ne ya katse mai tunaninsa da cewa " shaidu fa?"

Abdulmajid ya juya yace " shigo."
Nan wani bawa ya shigo wanda kowa ya sani bawa ne wanda ke kula da al'amuran Magajiya na waje bana ciki ba.

Daga can bakin kofa ya zube ya gaidasu, Abdulmajid yace " wannan bawan bawa ne ga Magajiya shi Mahaifiyar Abu Turab tai amfani gun aika mai da kaya dan gudun kar a gane itace."

To fa? Nan kowa yad'an fara magana kasa kasa.
Abdulmajid ya kalleshi yace " sanar damu abinda ka sani."
Muryarsa na rawa alamar tsoro da dana sani yace " tuba nake ranka ya dade amma abinda Yarima mai jiran gado ya fada haka yake, ranar nazo wucewa Baiwarta wato Lantana ta mikon kaya tace " dan Allah sauri nake dan mikama Abu Turab, basai ka shiga ba kawai ka bada a kofar shiga ka wuce."
Salati mutane suka fara dayawa sun gamsu dan sunsan ba yanda za'ai bawa yazo gaban mai martaba ya gilla karya haka.

Abu Turab yai murmushi sannan yace " Ammm ina Mai bada shaidar nan?"
Bawan yace ganinan Yarima."
Abu Turab yace " ka tabbata duk abinda ka fada gaskiya ne?"
Yace " hakan yake Ranka ya dade, ina ni ina karya gaban Takawa."

Abu Turab yace " haka ne, sai dai nima ina rokon a bani dama namai tambaya."
Mai Martaba yace " inajinka."

Abu Turab yace " inaso ka bani amsar tambaya ta cikin sauri ba tare da kaja min lokaci ba, inaso daga na tambayeka ka sanar dani amsa."
Kai ya daga.
Abu Turab yace " A ina kuka had'u?"
"Gaban Turakar Magajiya."
"Hmm kenan can ta bika saboda tana san ta aikeka?"
Muryarsa ce tadan sarke yace " banida masaniya akan wannan."
Yace " me yasa daka kawo kayan baka ce inji Lantana ba bayan a iya sanina wanda ya kawo kayan ance ya sanar da wanda ya aikosho?"
Inin na ya fara cikin tsoro yace " hmm hmm nima sauri nake hmm shi yasa....."

Abu Turab ya karseshi da cewa " ok na gane, saurin da kakeyi ne ya hanaka sanarwa ko?"
Da sauri yace haka ne.
Abu Turab yace " kenan bayi nane sukai karya tunda sun sanar dani an fada musu wanda ya aiko da kayan?"

Bawan yai shiru, Abu Turab yace " na fahimceka, yanzu tambaya d'aya zan maka, dakai da Lantana wanene yafi wani matsayi a gidan nan?"
Cikin rashin fahimtar zancensa yace " na fita."
Abu Turab yace " Good! Ka fita matsayi meya saka ka yarda ta aikeka?"

KAINUWA....Where stories live. Discover now