Kainuwa 52

6.2K 464 56
                                    


*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

_AyI hakuri da Jina shiru da kukai kwana biyu, azumi nakeyi_🙈

*52*

Abu Turab dama ya sanar da Fulani zancen tafiyarsa, nan sukai sallama da mai martaba cikin jin dadi dan bai tambayeshi dalilin tafiyarsa ba.

Sai da suka gama shiryawa tsaf sannan ya nemi ganin Bilkisu dan yin sallama.

Itakam Bilkisu tunda Munnira ta sanar da ita take tsaye tana zagaye d'akin, meke faruwa? abinda ke mata yawo kenan har mai kula da ita ta sanar da ita neman da Turab yake mata.

Cikin sauri ta duba fuskarta a jikin madubi sannan ta nemi fita, harta kai kofa sai kuma ta tsaya, taja wani dogon numfashi sannan ta kara neman nutsuwarta kafin ta fito.

Yana zaune yayi shiru ta shigo da sallama, dagowa yai tare da amsawa yana kallanta.

Sai data zauna sannan ta gaisheshi tare da cewa " Lafiya dai ko?" kallanta yai yace " nikaina abinda nake san sani kenan."
Kallan mamaki tamai sannan ta d'ora da cewa " badai wani abu mara kyau bane ya faru ko?"

Hannunsa ya sa yad'an shafi saman goshinsa sannan yace " Ina ji nane ba dadi, inajin kamar da wata babbar matsala datake faruwa a gida."

Kallansa tai sannan ta d'anyi murmushi tace " Insha Allah ba abinda ya faru sai alkairi, sannan in har wani abu mara kyau ya faru ko ka fuskanci kana cikin tsaka mai wuya ina rokonka da karka yanke hukuncin da nan gaba zakai dana sani, ka jinkirta yanke hukunci har sai zuciyarka ta aminta da wannan hukuncin."

Murmushi ya sakar mata yace " Nagode."

Itama murmushi tamai sannan ta sunkuyar da kanta kasa.

Mikewa yai yace " zan wuce."
D'agowa tai ta kuramai ido sai dai batace komai ba, a hankali ya tako zuwa inda take sannan ya tsuguna a gabanta tare da zaro abu a aljihu, ya nuna mata takardar databa Munnira na layin waya, yana murmushi yace " na gani na kuma gode."

Kallansa tai sannan ta saki wani lalausan murmushi.
Mikewa yai yace " kafin in dawo maybe an tsaida rana."

Da sauri ta maida kanta kasa, wata yar karamar dariya yai wacce batada sauti yace " wannan d'in kunya ce?"
D'agowa tai ta harareshi tace " dama haka ake yi? da kanka ya kamata ka fad'amin zancen?"

Dariya ya sakeyi yace "au haka ne? to goge abinda na fad'a a zuciyarki inyaso sai a sake sabon la le."

Murmushi tamai tare da juya kanta gefe tace " na goge." cikin zolaya yace " nikam me ma nace?"

Hararar sa ta sakeyi sannan ta maida kanta kasa tana murmushi, ashe yanada side na zolaya, farkon ganinsa ta d'auka mutum ne wanda bayasan wasa sam, sai dai yanzu ta fara tunanin tsauri da jinin mulki ne ya sashi haka.

Dagowa tai ta kalleshi sai dai batace komai ba.
Murmushi ya mata sannan yace " zan kira." kai ta d'agamai, yace " zan wuce" nan ma kai ta d'agamai.
Lab'ansa ya d'an hade sannan yace " nagode."

Murmushi tamai, nan ya juya yai hanayar fita.
Sai dayaje kofa yaji muryarta a hankali tace " Allah ya kiyaye hanya."
Juyowa yai yana murmushi yace " Ameen."
Nan ya juya ya fita, yana zuwa ya tadda Sabi'u ya sa an fita da komai, nan suka kama hanyar gida.

Basira kam abin duniya duk ya gama damunta tama rasa ina zata saka kanta, da farko tayi tunanin fad'ama Sarki sai dai tace me? wad'annan tunanin sun hanata sakat, fatanta kawai d'anta ya dawo, ta sanar dashi hukuncin magajiya.

KAINUWA....Where stories live. Discover now