Kainuwa......43

6K 488 57
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

_Tuba nake plz na jina shiru da kukai ✌🏻dayz_

*43*

Mairo ta tsaya kawai tana binsa da kallo, kai yad'an lank'wasar kadan yace " Lafiya?wannan kalan fa?"

Cikin mamaki ta amsa mai " Yaya Umma ta warke ne?"
Kai ya girgiza alamar a'a yace " baki taho mata da ganin bane? Ko samu ne ba'ai ba?"
Tace " to ko an gano gaskiya ne?"
Kallan rashin fahimta ya mata yace " menene?"
Tace " naganka ne kamar abin ya daina damunka, sannan idanunka suna d'auke da confidence."

Murmushi taga ya sakar mata yace " ni kaina bansan ya akai ba bayan nayi wata 'yar karamar waya na samu kaina cikin wannan yanayin."

Tana kokarin tambayarsa wace irin waya yai jitai yace " shiga ciki, inada abinyi."

Kafin tai kokarin magaa ma yayi gaba.
Komawa yai b'angarensa yai wanka ya d'auko kaya had'ad'u ya saka, shadda ce bugagiya light brown, yayi kyau sosai da sosai.
In har ka ganshi to fa lalai zaka d'auka wani taro na mahimmanci zaije.

Haka ya fito hankalinsa kwance, Garzali na ganinsa ya mike ya biyoshi yana tambayarsa inda zasu.
Turab yace " Bangaren Umma Babba zamu."

Bayan ya shiga ne yaga ragowar matan sarki da kuma matan kannansa a zazzaune suna gulmar abin, da alama dubiya sukazo suka bige da gulma.

Ganinsa yasa kowa ya ja bakinsa ya tsuke, Abu Turab fuskarsa d'auke da murmushi mai sanyi ya gaishesu, haka kowa ya dinga amsa gaisuwar a kunyace dan sun tabbata yaji me sukace.

Kowa sai dayai mamakin ganin yanda ya d'au kwalliya duba da yanayi da suke ciki.

Kwankwasa kofa yai, Khadija ta taso.
Tana tura kofar tai ido hudu da Abu Turab, tana rike da kofar take binsa da kallo, kallanta yai kallo na bege sai dai bayanda zaiyi, da sauri ta katse kallon da takemai tace " Barkanka da Zuwa."
Ta karasa maganar tare da matsamai ta bashi guri.

Magajiya ce a kwance kamar d'azu sai dai Abdulmajid na zaune a kasa yana cin abinci.
Murmushi ya saki sannan ya kalli Khadija yace " nima zanci abincin."
Da sauri Abdulmajid ya kalleshi dan da ya dauke kai dayaji muryarsa.
Khadija ta kalleshi itakanta tayi mamaki sai dai amsa mai tai dato, tai waje.

Abu Turab ya kara tura kofar ya shiga bakinsa d'auke da sallama.
Abdulmajid ko amsa mai baiyi ba sai kallan mamaki da yake binsa dashi, wannam kwalliyar fa?

Abu Turab ya karaso ciki ya zauna gaban Abdulmajid yace " Abdulmajid Barka da war haka."

Bai amsa mai ba sai kallan mamaki da yake mai.
Shima bai nemi amsar tasa ba Kallan Magajiya yai yace " Har yanzu Umman tamu bata farfad'o ba? Inata tsoro kar muje ta wuce ta can kasan matsalar guba akwai illa ta gaske."

Yanda yake maganar kai kace irin Abokinsa ne Abdulmajid d'in.
Abu Turab ya kalleshi yace " kayi shiru ko baka neman mata sauki ne?"
Abdulmajid ya saki wata dariya ta takaici yace " duk duniya inda wanda zai fi damuwa da ciwon ta ai banaji ya kaini ko?"

Jinjina kai ya shiga yi yana cewa " gaskiya ne kuma kayi magana anan, sai dai ni kaina ina mata fatan samun waraka, dan ciwonta duk ya hanani sukuni."

Mamaki da takaici ma sam ya hana Abdulmajid magana.
Abu Turab ya d'an furzar da wata iska yace " ta ina zanso Ummanmu ta gangara bayan ko bikina da Gimbiya Bilkisu bata gani ba? Sannan Bata ga d'anta akan mulki ba?"

KAINUWA....Wo Geschichten leben. Entdecke jetzt