Kainuwa....53

6.2K 476 40
                                    

*KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*53*

Har ya murd'a kofa sai yaji tace " Ahh na manta ashe akwai wacce kake so?"
Tsayawa yai cak sai dai a hankali ya juyo zuwa kallanta.
Murmushi ta saki tace " Hmm na kula da gaske ne, dama Khadija ce ta sanar dani akwai wacce kake so, nayi mamaki da naji haka da alama san mulki ne yasa ka ture wacce kakeso zuwa auran Gimbiya."

Idanunsa ne suka kad'a sosai Khadija?
Da karfi ya bud'e kofar ya fita cikin b'acin rai.

Magajiya ta bishi da harara tace " Mairon yakeso da gaske? Ko kuma akwai wata a kasa? Dama hakan ne yasa batace Mairo ba kai tsaye saboda tanaso taga yanda zaiyi, sai dai ta kasa ganewa."

Abu Turab tsaya wa yai a waje yai shiru, wata zazzafar iska ya fitar daha bakinsa yana kokarin juyawa ya ga Khadija ta taho.

Kallanta yai sau d'aya ya d'auke kansa, kalaman Magajiya ya maimaita na game da wacce yakeso, kenan kila na Khadijan har fada musu tai ita yake so? Wato gaba gaba amfani zasuyi da san da yake mata su cutar dashi? A da yana tunanin Khadija bazata tab'a cin amanarsa ba amma a yanzu ya cire wannan abun a ransa, bai san ta iso inda yake ba.
Sai jiyai cikin muryar tausayi tace "Yaya."

Kallanta yai fuskarnan tasa a d'aure tamau, ta d'auka jin abinda ya faru ne yasa shi cikin wannan hali, a hankali tace " Yaya kayi hak........"

Katseta yai da cewa " Alhamdulila banaji a yanzu zanyi kokwanto akan hukuncin da zuciyata zata yankemin, a da ina tunanin halin da zan sakaki, nagode kwarai da kika nunamin ke jinin Magajiya ce."

Yana kaiwa nan ya wuceta.
Sam ta kasa ma magana saboda ta kasa fahimtar abinda yake fad'a.
Ita datazo dan yima Abdulmajid magana da kara bashi baki akan ya janye maganar nan, me Turab yake nufi?

***********

B'angaren Mahaifiyarsa ya nufa, a zaune ya ganta ganin yanayin datake yasa yaji idanunsa sun ciciko, shiga yai ciki ya zauna sannan ya gaisheta.

Fuskarta d'auke da murmushin data kakaro tace "Turab akacemin ka dawo, nayi mamaki sosai ganin ba yau ne kace zaka dawo ba."

Mikewa yai jiki a sanyaye ya karaso inda take a hankali ya kwantar da kansa a kan gwiwarta idanunsa sun ciciko yace " Ba sai kin b'oye damuwarki ba a gabana Umma, na sani akwai babban matsala data kunno miki kai, ki sanar dani Umma ko na nemanr mana mafita."

Jitai hawaye na neman zubo mata da sauri ta mike tsaye ta juya mai baya tace " Ba komai Turab kawai dai jiya na d'anyi zazzab'ine shi yasa ka ganni haka."

Mikewa yai shima ya kalleta sannan yace " Me Magajiya take nufi da inzo ki sanar dani?"
Basira ta juyo tace " Haka tace ma?"
Kai ya d'aga alamar eh sannan tace "Maganar Abdulmajid ne da Mairo bayanshi banaji akwai wani abu."

Kallanta yai sai dai bai gamsu ba ya dai fahimci batasan yasan ko menene.
Juyawa yai yace "bari na koma ita ta sanar dani."
Cikin tsawa tace " Turab dakata."
Juyowa yai ya kalleta cikin yanayi na tausaywa yace " Umma kin manta wahalar da mukasha a rayuwa ni da ke? Kin manta matsala da tashin hankalin da kika fuskanta? Ta yaya zakiso ki b'oyemin wani abu?"

Idanu ta runste tace "Turab muna cikin tashin hankali, in har abinda Magajiya ta sani ya bayyana banaji zamu kara samun kwanciyar hankali a gidan nan."

Cikin shakkun kalamanta yace "Umma badai tasan maganar lahanin da aka miki ba?"

Kallansa tai hawayen dataketa dannewa suka zubo tace "Turab ya zamuyi? In har maganar nan ta fito ban san yanda mutane zasu kallemu ba, ba kuma naji za'a yadda da kai."

Idanunsa ne suka kad'a sosai lalai Magajiya bala'i ce yanzu mikin da ke b'oye a zuciyar matarnan sai data taso mata dashi hankalinta ya kwanta, lalai yaji dadi da mahaifiyarsa ta sanar dashi komai kafin rana irin ta yau, da bai san yanda zaiji maganar nan ba.

Murmushi ya sakar mata ko ince yake ya mata yace " Sai me Ummana? Iya kace mutane su gujemu to sai me?"

Kallansa tai cikin kunar zuci tace "kanaso kacemin baka fahimci me take nufi ba? In har magana ta fito zargin tsatson ka za'a shiga yi, in kuma ba haka ba sai dai kabi umarninta ka auri Mairo shikuma Abdulmajid ya auri Gimbiya."

Gani tai yasa dariya mara sauti yace " ohh wannan shine dalilinta?"
Basira ta kallshi tace " Kana tunanin Sarki zak taimakemu ko? Ka cire wannan a ranka in har kana wannan tunanin, Sarki ne shi kafin mahaifinka ko ince kafin ya zama mijina.'

Turab yace " Umma kin taba gani nace Sarki ya ya shiga ko ya taimakamin a yayin da matsala ta kunno min kai? Sai dai inje gun Abba na dan neman shawara, sannan maganar auran Bilkisu da Mairo duk wannan lamari ne na ubangiji Allah shine yasan matar da Abu Turab zai aura, Allah shine yasan ko dukansu zai aura, Allah ne yasab ko duk cikinsu ma ba wanda zan aura, sai dai nasan abu d'aya duk yanda zanyi bazan bar Abdulmajid ya auri Mairo ba saboda kamar kanwa take a gurina, sannan bazan bari ya auri Bilkisu ba saboda yarinya ce wacce bata cancanci miji kamar Abdulmajid ba."
Yana kaiwa nan ya juya zuciyarsa fal da bakin ciki.

Sam ya rasa ma ta ina zai fara.

Har bayan Magrib ya rasa mafita kawai ya nufi b'angaren Mahaifinsa.

Jakadiya ta matso ta gaisheshi sannan tace "Ranka ya dade Magajiya tana ciki."
Magajiya?
Ya maimaita yana kallan Jakadiya.
Jakadiya tai gyad'a kai tace "Sai dai ka dawo gobe inkuma kanaso in sanar masa."
Turab ya girgiza kai sannan yace "Barshi, sannan karki sanar mai da zuwana ko daga bayane."
Tace "to."

Harya juya ta biyoshi da sauri tace "Yarima."
Tsayawa yai sannan ya juyo ya kalleta yace"Lafiya?"

Daurewa tai tace "naji abinda ya faru, sai dai abu d'aya na isa fad'ama wannan abinda ta shirya reshe zai iya juyawa da mujiya, dan kuwa Magajiya tanada babban sirri duk abinda ake tunanin nata ne ba nata bane."
Turab ya kalleta cikin mamaki yace "Jakadiya ni fa......"
"Na barka lafiya Ranka ya dade, kai mutum ne mai zurfin tunani da kaifin basira zaka gano abinda nake nufi in har Allah ya nufeka da ganowa."
Ta juya tai gaba.
Da kallo ya bita sannan ya juya yai gaba.

*************

Abdulmajid wanda bayan shigarsa fada yana neman yin magana mahaifinsa ya mai wani kalli wanda kwarjini yasa ya kasa karasawa.
Ana magrib kuwa ya zari mota yai gidansu Mairo.

Tana xaune a waje ta kurama sararin samaniya ido tana kallan yanda yanayin duhun gari yake, yaro ne ya shigo yai sallama sannan yace " wai ana kiran Mairo."
Mairo ta kalleshi tace "inji wa?"
Yace "wai mijinki."

Kwafa tai sannan ta ciji lab'anta ta kuma mike da sauri, mayafita kawai ta zura tai waje dan ko Mamanta bata sani ba.

Yana cikin mota yana ganinta a tsaye a soro ya fito da sauri yana murmushin jin dadi.
Itama murmushin ta maida mai hakan yasa yaji kansa ya fasu.
Ya karaso gunta yace "Mairo na."
Tace "Yarima na."
Kallan mamaki ya mata sannan yasa dariya sosai yace "Mairo kece kuwa?"
Tace nice, kana mamaki ne?
Fuskarsa ya shafa cikin jin dadi sannan yace " Sosai ma "

Wani banzan kallo tamai tace "Kana tunanin haka zan ma in ka min ta karfi?"
Kallan tai yai yace "me kik....."
Katseshi tai tace " please Abdulmajid ka tashi daga wannan wawan baccin da kakeyi, wlh wlh in har ka kuskura ka dage da aurena har aka yi wlh ina tausaya maka da ni kaina dan a yanda nakejin tsanarka komai zai iya faruwa, dan wlh dana aureka gwara na auri talaka wanda bashida komai."

Jiyai zuciyarsa ta d'au zafi yace "Mairo how can u?"

Tace "me? Kana tunanin sunyi kadan kalaman nawa Busuru kawai, ka lalata 'yan mata sannan ka nemi auren wacce batasanka? Ko kana tunanin nima so na kake?"

Ta kalleshi cikin takaici tace "Aurena? Hmm please go ahead, a kaini gidanka inga ko zaka samu abinda kakeso."
Taja dogon tsaki zata juya.
Hannunta ya rike da sauri yace "Mairo taya zaki fadamin bakaken maganganun nan ki tafi?"

Ta makamai harara sannan ta kalli hannunta daya rike tace " sakeni ko?"

Kallanta yai sai taga ya sa dariya yace " Mairona in baki shawara? Ki bala'in kwantar da hankalinki ki aureni cikin farinciki dan wlh duk duniya ba wanda ya isa ya aureki sai ni nan Abdulmajid d'an Magajiya da Abdussamad."
Hannunta ta fizge tai cikin gida.

🤝🏻 *SASSANIN KUNGIYA TA ABU TURAB SADAUKI🏇🏻*

KAINUWA....Where stories live. Discover now