Kainuwa.....14

6.8K 509 31
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

_'Yan grp na Kainuwa Dashen Allah ga naku shafin, tnx 4 d love....._

*14*

Sun shirya tsaf ba kaya suka d'auka ba dan komai nasu anan tabarma matan gidan saboda tasan inda zasuje.

Shehu shi ya kawosu inda zasu hau mota dan a wannan shekara wato ta 1978 (shekarar Abu Turab 7 sannan shekararta takwas da aure.) a wannan lokacin an sanu cigaban wata yar kurkurar mota bayan akuri kura da motar itace, sai da suka shiga sannan Shehu ya musu sallama ya juya ya tafi, matansa sunsha kuka dan kuwa Basira ce silar zaman lafiyansu.

A hanya Basira sai kara jaddadama d'anta takeyi akan abinda takesan yayi.

Daga baya bacci yai awun gaba dashi, Lantana ta kalleta sannan tace " Ranki ya dade inasan tambaya duk da dai ba hurumi na bane."

Basira ta kalleta alamar tana ji, Lantana tai ajiyar zuciya sannan tace " me zakice ya hanaki komawa? Dan ina tsoron kar a miki wani sharrin."

Basira tai murmushi tace " Lantana kenan, a da na yarda ni sukuwa ce wacce bata tunanin abinda zai faru, sai dai yanzu inada abinda nakesan karewa dolene in canza daga sukuwa zuwa nai dabara, karki damu." ta karasa maganar tare da dafata.

Sun dade suna tafiya kafin a d'an tsaya saboda wasu yaran na mota najin fitsari, nan fa aka fifita hardasu Abu Turab, bayan an dawo ne aka ci gaba da tafiya.

Sai yamma lis suka isa garin na Zariya.

Basira bayan sun sauka ta kalli Lantana tace "zaki iya gane gidan da na fara zama?"

Kai ta kada mata alamar eh, ta d'aura da cewa "sosai kuwa."

"Can zamu wuce."

Ba tare da tambaya ba Lantana ta amsa da to, Abu Turab ya rike sandarsa kamar yanda mahaifiyarsa ta umarceshi, dayake dama idanta a bud'e yake tarau a da d'in ma sai ance miki baya gani tukunna dan in kika ganshi haka bazakiyi tunanin rashin ganinsa ba.

Haka sukai ta tafiya har suka isa gidan, dan ma ba nisa sosai.

Suna isa suka karasa bakin kofar da fadawa biyu ke gadinta, Lantana ta kallesu sannan ta musu gaisuwar da take nuna alamar a masarauta take, sannan ta d'aura da cewa " Matar Mai Martaba ce Gimbiya Basira."

Kallan juna sukai alamar basu fahimta ba, dan kuwa su basu santa ba, ba'a dade da kawosu nan ba, sannan ko da ace ma sun santa ai shekarun dayawa dan kuwa mutane dayawa sun manta da ita, wasu sai da insun tunata susa dariya, wasu kuwa suyi tunani ko tana raye?

Basira ce ta kallesu tace " bud'e mana, shiga zamuyi sannan d'aya ya zauna dan ya tabbatar da mudin ba da wani nufi mukazo ba, sannan d'aya yaje Fada ya sanar da Mai Martaba yayi baki na sirri anan."

Kallan mamaki suka mata, Basira ta kalli na hannun dama tace " naga kamar kai bazaka iya mana komai ba in ma munzo da wani nufi ne, ganin yanayinka, dan haka so nake kaje ka samu sarki in ba hali ka samu Barde kace ya sanar da Sarki a kwai bakin sirri a gidansa na cikin gari."

Kallanta yai yana kokonto, Basira tace " kada ka kuskura ka sanarma kowa sai mutanen nan biyu, ganin kafin kaga Sarki abin zai zama mai wuya ina shawartarka ka sanarda Barde, kada ka fadama kowa inba shi ba."

To, ya fada yanzu kam ya fara yarda da sunsan mai Martaba duk da dai bai yarda matarshi bace sai dai gani kamanni iri na Abu Turab yasa ya san tabbas akwai hadin jini na sarki a jikinsa.

KAINUWA....Where stories live. Discover now