Kainuwa.......24

6.5K 505 33
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*24*

Abu Turab yana shiga d'akinsa ya rufe tare da jingina a jikin kofar, tausayin Mahaifinsa ne yake ratsa jikinsa ace kana san abu amma saboda kana mulki baka isa ka nuna ba? Lalai shikam wannan mulkin sam baya kansa.

Haka ya kwanta bacci zuciyarsa fal da tunani kala kala.

********

Washegari a fada Mai Martaba ya umarci Abdulmajid akan ya d'aurashi akan aikin binciken abinda ya samu kaninsa.

Ba Abdulmajid ba kowa na fadar sai da yai mamakin wannan al'amari, ai ko ba'a fada ba kowa yasan ba wata soyayya ko mutunci a tsakaninsu, amma ace shine zaiyi binciken?

Andulmajid ya kalli Mai Martaba cikin tsananin mamaki, kafin ya daure yace " insha Allah zanyi binciken abin in sanar maka."

Yana fitowa Hisham ya biyoshi, Hisham ya kalleshi yace " me ke faruwa?"

Abdulmajid ya dan kurama kasa ido sannan yace " abinda ke faruwa?" Umm yad'anyi ajiyar zuciya yace " wannan shine tambayar da zan fara nemanma amsa."

Hisham yace " muje gun Magajiya nikaina inasan ganinta."

Bayan sun isa gunta ne sun gaisheta, Abdulmajid ya sanar da ita abinda ke faruwa, murmushi ne mai sanyi ya bayyana a fuskarta ta kalli d'an nata tace " hmm lalai Turab ya girma sai dai Tsohon doki yafi sabon takalmi."

Abdulmajid ya mata kallan rashin fahimta, "Tsi tsi tsi tsi" abinda tai da bakinta kenan tana jijiga kai tace " karka badani mana Abdulmajid, ba shakka Turab abinda ya nema mahaifinsa yamai kenan jiya.

Hisham yace " nima naji labarin zuwansa sai dai naji ance fada aka mai?"

Baki ta tabe tace " ko da wasa ni nasan ba fada aka mai ba in har fada ne mezaisa ya shiga kuryar d'aki? Sannan da yamma ya riga ya umarci Sabi'u akan yai bincike sannan yau da safe ya maidashi kan Turab ne hakan yake nufi?"

Hisham ya kalleta yace "amma hauka yake da zai umarci Abdulmajid? Bayan yasan ba sanshi yake ba."

Abdulmajid ya kalli Magajiya yace " Umma kina nufin yayi hakan ne saboda karmu d'aurama mahaifiyarsa laifi? Tunda yasan ai ni ban isa ince mahaifiyarsa bace hakan zaisa a zargeni."

Magajiya ta mai alamar jinjina da hannu tace " kwarai kuwa Yarima na ashe ka harbo jirgin."

Dariya Abdulmajid yai yace " lalai yaran nan, yana makaho har......"
Katseshi tai tace " munyi sakaci da muka ragamai muna tunanin makaho ai baya ganin komai, masarauta fa muke?sannan jinin mahaifinsa da kakansa suna yawo fa ajikinsa."

Hisham ya kalleta yace " yanzu meye abinyi?"

"Hmm farko dai tunda ya maida wasan kanmu dole ne mu buga wasan, ai hakorin dariya shi yakanyi cizo."

Kallan mamaki suka mata, tai kalli Abdulmajid tace " ka nutsu sosai kaga yanda zan buga wasan."

Shiru yad'an biyo baya kafin Hisham yace " ni kuma wani abu d'aya ne yake damuna, me yasa haryanzu sarki ya kasa neman ma Abu Turab magani?tunfarkon zuwan sa da yadanyi na shekaru kad'an yanzu sam baya turo masu magani, ko ya hakura ne da makantar yaron....."

Magajiya ta d'an kankance ido tace "ko kuma ya warke ba."

Idanu suka zaro suka kalleta, shiru tai tana tunani kafin ta mike da sauri tace " me yasa hakan baizo min ba?"

Da sauri ta kalli Hisham tace " Hisham aika a kiramin yaron nan."

KAINUWA....Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang