Kainuwa......46

6.2K 527 20
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

_Ina 'yan group na fans d'in kungiyar Haske Writer's? Ina kuke 'yan group d'in The Queen Bee? Ga taku sadaukarwar, wannan shafin sadaukarwace gareku....🤝🏻_

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🏌🏻‍♀*

*46*

Jakadiya ce tazo dan kaisu inda aka tanada dan ganawarsu, an kayata gurin sosai, gun kamar rumfa yake, salo da kayata gun da akai duk yanda kaso da karka nuna sai gun ya burgeka.
Gashi sai hayaki na turaren wuta ne ke tashi.
Sabi'u cikin mamaki yake kallan gun ya kalli Turab wanda shikansa abin ya kayatar dashi yace " Kai gun nan ya burgeni, amma dai ba dan kai aka shirya gun nan ba ko?"
Abu Turab ya kalleshi yace " kai kuma sarkin zuga zugi, to kardai ka wuce makad'i da rawa."

Sabi'u ya kara shan mamaki ne a sanda yaga yanda aka saka irin carpet da 'yan tumtum a gun sannan aka jera kayan ciye ciye kala kala, ya jinjina kai yace " Turab da alama gaisawa kawai zamuyi da Bilkisu banaji anyi wannan shirin dan mu biyu."
Cikin gatse Turab yace " Gaisuwar ma sai ka hakura."
Sabi'u yace " ahh lalai Turab abin ba kara? To bari inje waje in tsaya in yaso in kungama ganawar na shigo daga baya mu gaisa."

Turab kai kawai ya girgiza, ya juyo da niyyar mai magana yaga bayanan.
D'an tsaki yaja kad'an yace " Sabi'u kenan."

Zama yai a gun da aka shirya dominsa, irin zama na manyan 'ya'yan Sarki.

Sai dayai minti 15 da zama sannan wani dadadan kamshin turare ya bugi hancinsa.
Cikin isa da takama take takowa, tafiya takeyi irin ta kasaitatun mata masu mulki.

Bai d'ago ya kalleta ba haka itama ko data shigo kallo d'aya ta masa ta cigaba da takunta.

Har sai da ta iso gun da zata zauna sannan ya d'ago ya kalleta, itama a lokacin ta kalleshi.

Tabbas yarinyar tana da kyau, balle yau datai shiga mai kyau sosai sannan tai kwalliya haka, wani sansanyan murmushi ta sakar masa, shima murmushin ya maida mata, a hankali ta zauna sannan ta umarci bayinta dasu fita.

Shiru ne ya ratsa gun kafin cikin muryarta mai dadi tace "Barka da isowa Yarima Turab."

Kallanta yai cikin yarda da amincewa yace " Barkanki da isowa Gimbiya Bilkisu."

Murmushi tai sannan tace " ka dade a zaune ko?"
" Ya zama dole ai in jiraki tunda haka tsarin yake, sannan ba wani dadewa nai ba."

Bata ce komai ba sai shiru da suka sakeyi.
Kanta na kasa, batai zato ba sai jitai yace " Bilkisu." Yanda ya kira sunanta sai dayasa taji wani yarr a jikinta.

D'agowa tai a hankali ta kalleshi idanunta sun canza zuwa salon soyayya, murmushi yai yace " Naji dadi da yanda kika amince da ni."
Idanunta ta lumshe sannan ta bud'esu.
Yacigaba " ban taba zatan zaki yarda dani ba haka, duba da rashin sani na da kikai, tunda haduwarmu d'aya dake."

Nan ma idanunta ta kara lumshewa ta bud'e, yace " A wannan lokacin na sa ma raina tabbas zaki zama mace ta gari a gun duk wanda kika aura, sannan na yaba sosai da yanda kike da tunani."

Murmushi ta saki sannan ta maida kanta kasa, hannayenta ta had'e gu d'aya tana murza zoben hannunta da d'aya hannun.

Harya d'auka bazatai magana ba sai jiyai tace " I can feel the pain that hide behind ur smile Turab."

D'agowa yai ya kalleta sai dai jikinsa yai sanyi, kallansa tai tana murmushi tace " me zakace game da ni?"

Kallanta yai kallo mai alamar tambaya.
Kanta ta d'an karkatar tace " ka taba sanin Fulani ba ita ta haifen ba?"

Idanunsa ne suka fifito alamar mamaki, Tace " bansan ta ba, bansan ya kamanninta suke ba, tana haifata a gun Allah ya mata cikawa."

Tausayinta ne yaji ya kamashi.
Idanunta ne suka d'an ciciko tace " karka kallan da fuskar tausayi Turab, i am okay, tunda dadewa na cire san ganinta a raina, sannan ina ganin in har na nuna damuwata akan mahaifiyar data haifen ya Fulani wato mahaifiyata ta yanzu zataji?"

Turab ya kura mata ido yana nazarin kalamanta. Can yace " U are indeed a good woman, sai dai jin zancen nan naki yasa na fara tunani ban kai qualification na aurenki ba, kin cancanci saurayin da zai soki kamar ransa wanda zai kula dake har rabuwa ta rai ta zo."

Hannu tasa ta goge hawayen daya d'an gangaro ta kwarmin idanunta tana murmushi tace " kai bakada confidence na sona kamar haka?"

Jitai yayi shiru sai dai yanayin kallan da yake mata ya canza, kallansa tai tace " Me kake nufi?"

Yace " Bilkisu inada abubuwa da dama a gabana wanda sai na ga sun kammala ne hankalina zai kwanta, banida lokacin soyayya ko farin ciki sai na ga mutanen nan an musu hukunci."

Shiru yai dan tuno abinda aka ma Mahaifiyarsa.

Baiyi tsamani ba bai kuma ji alamun tasowarta ba sai gani yai ta mikomai kofi.

Kallanta yai idanunsa sunyi ja, sannan ya kalli kofin ruwa ne a ciki alama tamai da kai akan ya amsa.
Hannu yasa ya amsa yana murmushi, yace " sry......"
Katseshi tai tace " naji dadi."

Fuskarta d'auke da murmushi tace " naji dadin yanda ka nunamin, yarda harka ke sanar dani hakan."

Kofin ya ajiye bayan ya shanye ruwa ciki yace " Bilkisu i....."
Kara katseshi tai tace " is okay, na fahimceka, na kuma san tabbas akwai wahalhalu da kasha ko fansar wani abu da kake san d'auka, sai dai inaso in taimakeka gurin d'aukar wannan fansar, bazan nemi soyayyarka ba har sai ka kammala abinda zakai, sai dai kaima bazan yarda kaso wata ba har zuwa wannan lokacin, in kuwa har da wacce kakeso yanzu inaso ka ajiye soyayyar a iya kacin zuciyarka harsai ka gama aiwatar da abinda zakai, a wannan lokacin ne nakeso ka tambayeni abu d'aya."

Idanunsa na kanta tacigaba " inaso ka tambayeni in har banyi dana sanin auranka ba, in har nace ma banyi dana sani ba to inaso ka tirsasa zuciyarka ta soni in har aka kai wannan lokacin baka sona, in kuma har nace nayi dana sani inaso ka tambayeni abinda nakeso a wannan lokacin."

Tana gama fad'ar haka ta koma ta zauna sannan ta d'ago ta kalleshi tace " Deal?"

Bai san sanda wani murmushi ya bayyana a fuskarsa ba yana murmushi yace " Deal! sannan naji dadi da kalamanki, ba saki a tsarin aure na ko da shi kike tunani a karshe sannan yanda kika amince dani ba tare da kinji abinda nakesan aikatawa ba, zanyi kokari wajen ganin bakiyi dana sanin aurena ba."

A tare sukama juna murmushi nan tamai alama da hannu akan yaci abinda aka kawo masa.

Tabbas tana bala'in san yaran nan, ko da kuwa zatai dana sani akan auransa bataji zata iya rabuwa dashi a wannan lokacin, sai dai ta d'au alwashin taimaka mai da tayashi d'aukan fansa akan duk wani wanda ya cutar dashi ko da kuwa zatai amfani da karfin mulki na mahaifinta ne.

Kamar yasan me take tunani jitai yace " for using you, dole ne ma nemi yafiyarki, sai dai zan nemane in na gama komai, is that okay?"

Kai ta jinjina mai alamar eh, ta bishi da kallo na so tsantsa.

Bayan sun gama hira ne ya mata sallama sannan ya mike, har ya fara tafiya sai kuma ya juyo ya tako a hankali zuwa inda take.

Awarwaro ya ajiye mata wanda suke cikin gidansu sannan cikin magana mai kama da rad'a yace " da kunyar badawa nakeyi, sai dai bani na siya ba Sabi'u ne ya siyo"
Mikewa yai ya fara tafiya, kallansa tai tana murmushi tace " nagode."

Bai kara magana ba yai gama yana murmushi.
Tabbas Bilkisu ta samu daraja a idanunsa, yanaji zai iya zama da ita a rayuwar aure dan dama ya ma cire burin ganinsa da Khadija daga sanda yaji abinda mahaifinta ya musu ko da santa zai zama ajalinsa bazai taba yarda ya bakanta ran mahaifiyarsa akan 'ya mace ba.







*🤝🏻TEAM TURAB*

KAINUWA....Where stories live. Discover now