Kainuwa.....19

6.9K 485 14
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _ɖąʂɧɛŋ Διιąɧ_
( _*A Historical Fiction*_)

*H̝a̝s̝k̝e̝ W̝r̝i̝t̝e̝r̝s̝ A̝s̝s̝o̝c̝i̝a̝t̝i̝o̝n̝*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*ŋą Ä̤ʏʊֆɦɛʀ ʍʊɦɖ🤸🏼*

*19*

Da yamma suka shirya ita da d'anta dan zuwa gaida Magajiya.

Duk inda sukai kallansu ake ana 'yan gulmace gulmace har suka isa b'angaren Magajiya.

Tana kilisarta itada d'anta, bayan an neman musu izini nan suka shiga,ta kama hannun Abu Turab sakamakon sakeshi da Lantana tai da zasi shiga.

Abu Turab ya sauke idansa akan hamshakiyar matar dake zaune ta kafe kofar da sazu shigo da ido.

Kallanta yai sannan ya kalli d'an nata dake gefe sai kuma yai kasa dakai.

Magajiya kam ta kafeshi da ido tunda suka shigo har suka isa suka zauna.

Ta rasa me yasa tana ganinshi taji gabanta yayi wani wawan fad'uwa, Basira ta kalla sai dai yanzu taga alamar ba tsoro da gidadanci a idanunta kamar waccan zuwan nata na da.

Zama sukai,Magajiya ta kara kallan yaron a ranta tace " sak Mai Martaba lalai naji dadi da Yakumbo ta taimaka wajen nakasa idan nan."

Gaisheta Basira tai, i
Bata amsa ba ta maida idanta gun yaron, ya d'ago suka hada ido da sauri ya kalli gefe yace "Barka da Yamma."
Tabbas tasan sun hada ido sai dai dayake zuciyarta na farin ciki da kasancewarsa makaho yasa ta kasa dogon nazari akan haka.

Abdulmajid kam ya had'e rai da alama bashida niyyar gaida Basira.
Sai da Magajiya tace "Yarima baka gansu bane?"
"Barka."
Abinda ya fada ma Basira kenan.

Murmushi tai ta kalli Abu Turab tace " Yarima bakaga yayanka bane?"

Wannan kalma ta ba Magajiya da Abdulmajid mamaki, yarima? Haryaushe yazo?kuma ma a gabansu?"

Abi Turab bai kalleshi ba yace "Barkanka dai Yarima."

Magajiya zatai magana, Basira tai saurin cewa " haba Abu Turab sai kace ba yayanka ba? Ai kai basai ka kirashi Yarima ba ko Magajiya?"
Ta karasa maganar tana kallan Magajiya.

Magajiya ta juya ido a ranta tace " lalai wai so kike ki nunamin kin kile ko me?"
Murmushi ta saki sannan tace " hakane abinda kika fada sai dai kinsan tsintaciyar mage bata mage."

Basira cikin mamaki tace "bangane ba?"

Magajiya tai wani nishi na kasaita tace " Dafatan muhallinku an sa komai da komai? Dan ina nan ina fama da al'amuran cikin gida ban samu naje ba."

Basira ta daure tace " komai yayi."

Shiru suka d'anyi Magajiya na kallan yaran, can tace " naji ance ka fita riga a yage jiya? Meke faruwa? Ko dayake laifinki ne kinsan yaran makaho ne bai kamata ki barshi shi kadai ba."

Basira ta kalleta kadan batai magana ba,BU turab yai saurin cewa " Laifinane dan batasan ma nafita ba."

Magajiya a hasale tace " kada ka kuskura in inamagana da mahaifiyarka kasamin baki, ko kaga Abdulmajid na haka? Wannan alama kake nunawa na kataso a wani gun daba Gidan sarauta ba."

Basira ta kalleshi tace " kada ka sake, sannan yi maza ka bata hakuri."

Shiru Abu Turab yai wanda hakan yasa Basira tai dana sanin cewa ya bada hakuri, tasan halin d'anta sarai inhar tace yai abu ya tsuke baki to fa lalai bazaiyi ba.

KAINUWA....Where stories live. Discover now