Kainuwa.......16

7.1K 407 13
                                    

🕊 *KAINUWA*🕊
......... _Dashen Allah_
( _*A Historical Fiction*_)

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*

*Wattpad :-AyusherMohd*

*Na Ayusher Muhd🤸🏼*

*16*

Yau da sassafe kafin Mai Martaba ya tafi bada a aika a kira masa Magajiya.

Zama tai irin yanda ta saba sannan ta kalleshi, ba sai an fada mata ba ta fahimci magana yakesan yi mai mahimmanci.

Ya dade baice komai ba kafin ya ja numfashi yace " Magana nakeso muyi, ko ince abu nakesan fada miki."

Kallansa tai sannan ta maida kanta inda take kallo da.

Sarki ya nisa yace " akwai abinda na b'oye miki ko ince akwai abinda ya kasance sirri na ne da ba wanda ya sani."

Bata juyo ba dan bata taba kawo wani abu ne babba ba, Sarki yacigaba " Matata da d'ana zan maido gidan nan zuwa gobe."

Da sauri ta juyo ta kalleshi tana mamakin kalamansa dan sam bata fahimci ina ya dosa bama.

Sarki ya cigaba da cewa "Matata da ke zaune a cikin gari d'aya daga cikin gidajena, uzuri ne yasa take zaune acan saboda d'an data haifa ya kasance yanada lalura, wanda hakan yasa ta naimi zama acan dan ta kula dashi, ba wai dan tana tunanin nan din bazai samu kulawa ba a'a sai dan lalurar tasa babbace wacce take bukatar kulawa."

Tunda ya fara maganar take bin bakinsa da kallo dan ta kasa aminta da abinda kunnenta ke ji.

Daurewa tai tace " aure kai bamu sani ko me? Nifa na kasa fahimtar inda ka dosa."

Kallanta yai yace " Basira nake nufi da d'ana Abu Turab wanda suke gidana shekara bakwai kenan."

"me kace? Basira da d'anta?sannan suna zaune a gidanka shekara bakwai? Takawa mai kake san cewa ne?"

Mikewa yai yace " ana jira na a fada, sannan na tabbata zakiji abin banbarakwai sai dai gaskiyar kenan." kasa magana tai saboda tsananin mamaki, tana kallo ya juya ya fita.

Shikam ya sani in har ya mata lago lago tabbas sai ta bulomai da wani abun.

Ta dade a zaune kafin Ta mike tai bangarenta.

D'aki ta shiga ta rufe, tafiya ta dinga yi a d'akin cikin tashin hankali, me ke faruwa? Meke faruwa?

Ta dade kafin ta aika a kira mata Hisham.

Hisham kam ya taho ko a jikinsa dan dama yanasan ya mata magana akan a nad'a dansa matsayin Yarima mai jiran gado sai kuma ta aika a kirashi.

B'angaren d'ansa ya fara zuwa, yana shiga yaji alamar fasa abu, da sauri ya shiga ciki hankali a tashe.

Abdulmajid ya gani a zaune ga bayinsa sunsa gwiwowunsu a kasa suna bashi hakuri, a hasale Abdulmajid ya kallesu yace " ba nace banasan a kawomin ruwa a irin wannan kopin ba?"

Hakuri suke bashi hankalinsu a tashe, ya wani juya kai irin ba saukin nan yace " bazai yiwu ba Ummana zan sanarwa ta d'au mataki a kanku."

Nan suka shiga rokonsa, Hisham yai dariya ya juya ya fita yana jinjina kai, murmushi ya saki yace " haka akeso ai, gwara ya nuna musu a kasan sa suke hakan zaisa inya zama Sarki a dinga tsoronsa."

A zaune ya tadda Magajiya sai dai kana kallanta kasan tana cikin tashin hankali, nan Hisham ya d'an tabe baki kadan yace "wa ya tabo wannan zakanyar?"

Kusa da ita ya karasa ya zauna yace " Magajiya menene?"

Ta kalleshi cikin tashin hankali sannan ta bada umarni a basu guri, kallanta yai sannan yai dan dariya yace " menene? Khadija tace a gaisheki."

KAINUWA....Where stories live. Discover now