*~Based on True life story~*
NABEELA
*🤍(RAYUWAR AURENA)🤍*BY THE DMKs✍🏻
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
~Wanan Labarin is based on True life story~✍🏻
Page 57
@ Mambilla
Wai ke kam HADIZA wai mai ke damun ki ne haka duk kin lalace saikace ba ke ba Aradu ALLAH bacin na miki kallon tsab da sai nace bake bace
Hehehe Yo dole kinga ta a haka.. Matar da ta gama siyar da duk wani kadarorin ta wai zata yi kudin jigir ta tafi amurika niman WALIYE in banda abin HADIZA inata ina zuwa amurika ke ni koh hajji nan da Tace taje ban yarda ta je ba
HASSANA ya ishe ki haka Aradu ALLAH in bahaka ba zan sauke miki duk abinda ke kaina
Hehehe sauke shi nace in ba ki sauke ba kin Raina kanki kinji koh
Haba HASSANA bai Kai ga haka ba
Toh ANDE wai ma hauka akeyi ace wai da lafiya na da komai wanan matsiyaciyar Matan tana gayamin magana Sai kace ni na cinye mata kudi zuwa amurika.. Nan nan Ammadu yasani da Hyre zuwa kano gidan WALIYE Amma akace mana basu dawo ba
Amma da yake matan nan bata da mutunci bata gada mutunci shine zata dinga gayamin maganaAyi Hakuri HASSANA abin bai Kai haka ba..
ANDE kinji ki zo mushiga daga ciki
Oh wani munafinci za a Gila mata ah bashaka toh sai ayi mugani
ANDE dama Aramin kudi zakiyi dubu Ashirin zuwa karshen wata
Hehehe Yau kece da tambaya Aron kudi? Ah lallai bashaka abin mamaki duniya kenan tayi maki juyin mage
ANDE kinji nasa gona na a kasuwa Kuma ance Sai karshen wata
Toh badamuwa ki aiko anjima
A'ah yanzu ma Sai na biki na amsa
Toh shikenan
Yau wa gari ya waya anzo ana mana birgan banza da na hofi akan kudin iska
HASSANA ya ishe ki bawai gazawa nayi ba kudin ne baya hanuna Shiyasa kinji koh
Toh ina kudin suke? Kowa yasan babu duk birga ce da dashi ai baza a siyar da kadarorin ba hehehehe ALLAH nagodai
Toh an siyar in daice nawa ne bana wata katuwar ba
uban wa kk kira da katuwa eh? kinfa san halina wollah yanzu nan na murje ki a banza
Haba HASSANA ai girma yazo ai bama zai Kai ga haka ba Kuyi Hakuri Don ALLAH kinga mallam na kwance ba lafiya kar kusa shi cikin damuwa Kuma
Haba ANDE Kema Kisan Bazan biye mata bale mu tada mallam daga barci
Toh ki ma biye kigani in ba karyaki ba Yo hauka ma akeyi da za ace da lafiya na da komai wanan matsiyaciyar Matan tana gayamin magana Sai inyi sololiyo ina kallon ta kuma maganar mallam da kk yi kin damu dashi ne? Yaushe rabon da kije ki dubashi tunda yafara ciwon nan eh... Sai kinga mutane kifito kina mirsisi da ido kamar an murje gyada wai ke mai tausayi koh
Aradu ALLAH kifita idona na rufe
In naki fa? Mai zakiyi eh HADIZA? Nace mai zakiyi?
ALLAH ya baki Hakuri
Amin. Ai nadauka Magana zakiyi da kinji ki a kasa wollah
ANDE muje toh kinji
Toh HASSANA sai ALLAH ya kaimu ALLAH ya bashi lafiya yasa kaffara ce amin

YOU ARE READING
NABEELA(RAYUWAR AURENA)
Non-FictionWanan Labarin Is based on True life story.. " "Labarine da ya kunshi abubuwa da dama akan Rayuwa da zamantakewa Auretaya" "Labarin Wata yarinya Yar shakara sha shida aduniya wacca ta taso a hanu kishiyoyi mamanta Alokacin da take tunani cewa wahal...