Page 24
Godiya ta musamman ga UMMINRASHIDA CARE FOUNDATION, saƙo ya iso gareni, ina muku fatan alkairin nima, tare da godiyan bangirma da jinjina, alkairin ALLAH yakai gareku aduk inda kuke. Nagode da wannan girmamawa taku a gareni, duk da har yazu dai bilyn Abdull rarrafe takeyi, Inai muku so irin trillions ɗinnan😍😍😘😘👍🏻
................Jin Alhaji baba ya fara sauke numfashi Jawaad ya buɗe idanu a hankali, juyi yay domin ya tabbatar barcin baba yay nisa tamkar a cikin barci yake, shiru baiji Alhaji baba ya motsaba, yay murmushi tare da sauka daga gadon a hankali, cikin sanɗa ya fito daga bedroom ɗin, a falonma yanayi yana waiwaye harya fice, gudun matsala yasa yabar motarsa anan ya fice daga gidan baki ɗaya, wayarsa ya ciro a aljihu ya duba time, sha biyu saura kwata, ya maida wayar a aljihu yana furzar da iska. Daga gidan zuwa titi babu nisa sosai, hakan yasa ya taka da ƙafa ya samu napep. Saida suka fara tafiya ya sake fiddo wayarsa ya duba saƙon su Jabeer daya shigo tun ɗazun, ɗan typing yayi kaɗan ya tura musu cewar gashinan a hanya.
Cikin mintuna kaɗan suka iso gidansa na A.Y, sai dai bai bari sun ƙarasa gidanba ya sauka, dubu guda ya miƙama mai napep, yana ya tsaya ga canji amma Jawaad bai saurareshiba yay wucewarsa. Mai napep ya cusa kuɗinsa a aljihu yana faɗin “gaba ta kaini inma bakasan ka baniba”.
Oho Jawaad baisan yanaiba, tunima ya shige gidan. A falo ya iske su Aliyu, kowa da hidimar da yakeyi, ya zauna cikin kujera yana faɗin, “Kuyi haƙuri na rikeku anan ga madams suna jiranku a gida”. Hafiz dake aiki a lap-top yace, “Babu damuwa ango, yanzu dai mike faruwa?”.
Ajiyar zuciya Jawaad ya sauke yana faɗin, “Akan abinda ya farune yau, nasan kuma duk a ƙage kuke da sonjin yadda akayi?”.
Hakane boss. Suka faɗa a tare idanunsu na akansa.
Bayansa ya jingina da kujera yana mai ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya, cikin ɗacin murya yace, “Kamar yanda nasan tunaniku na akan nine na canja komai hakane, nayi ne saboda labari dana samu daga majiya mai ƙarfi akan abinda Momy ta ƙulla ita dasu mama Atika. A zahiri sun tsaida bikin Qaseem ne da yarinyarnan Miemaa, sai dai a baɗini sun tanadarma Qaseem mata batare dashi kansa ya saniba. Azeemar da aka ɗaura aurensa dashi ɗiyace ga Gwaggo Hajarah ƙanwar Momy da suke ɗaki ɗaya”.
Sosai mamaki ya cika zukatan su Jabeer, Hafiz yace, “To amma miyasa sukai hakan?”.
“Wannan itace amsar da nakeson mu nemo nima Hafiz, har yanzu mamaki baibar ɗawainiya da zuciyataba akan wannan al'amarin, miyasa zasu aurama Qaseem Azeema bayan sunsan ga wadda yace yanaso?”. Jabeer yace, “Nidai a nawa ganin kamar dama basason aurensa da Mami ne, sunsan kuma kosun hanashi bazai hanuba, shine suka zaɓi bi ta bayan fage su haɗa masa guda biyu, zaɓinsu da kuma nashi zaɓin”. Hafiz yace, “Maganarka akwai ƙamshin gaskiya Jabeer, to amma idan hakane shi Habib ɗinan miya kawosa cikin wannan al'amarin, sannan wanene shiɗin kuma?”.
Aliyu datun ɗazun baice komaiba yay ƙwafa, “Ni wlhy kusan kawai minake saƙawa a wannan lamarin kuwa; Duk kallonsa sukayi suna jiran ƙarin bayani. ya cigaba da faɗin, “Inagafa su sun tsara al'amarinne akan boss ya auri Shahudah, Qaseem a bashi Azeema, ita kuma Mami su aura mata Habib ɗin, inhar ba hakanne tsarinsuba miya kawo shi habib ɗin a zancen tunda alama ta nuna babu matarsa a cikin list ɗin ɗaurin auren?”. Zaune sosai Jawaad ya tashi idanunsa akan Aliyu, yace, “Aliy wannan maganar taka haka take, abinda yake cin raina anan inhar hakanne to kenan shi Dad bai fahimci Mom batason aure Miemaa da Qaseem ba kenan? Kokuwa shima ta shirya cin dunduniyarsa ne? Tunda ɗiyar ƴar uwarsa ce”. Hafiz yace, “To nima dai abin yasani wannan hasashen, amma kuma idan mukai dubi da yanda ya tada hankalinsa bayan faruwar abun harda suma hakan na nufin baisan su Momyn Shahudah sun shirya hakanba?”.
Shiru duk sukai suna nazarin maganar Hafiz ɗin, Jawaad ya miƙe tsaye hanayensa duka cikin aljihun wandonsa, kallo ɗaya zakai masa ka fahimci ransa a ɓace yake, yace, “Basu kaɗai suka shiryaba, hardasu Uncle Nasir, abinda yasa abin ya tsayamin arai shine, miyasa shi Uncle Nasir zai zama munafuki a tsakaninmu? Shinefa ya jagorancemu wajen Dad ni da Alhaji baba akan maganar Miemaa ɗin, saboda Ummah ta matsa akan sai dai Alhaji baba ya nemamin aurenta tare da Hudah kodan hakan ya zama gargaɗi gareta, kenan yasan shirinsu da Momy, amma kuma ya amsama Alhaji baba cewar muje muyima Dad ɗin maganar a haɗamin auren Miemaa da Hudah? Sannan sarai yasan Qaseem an tsaida masa ranar aure da Miemaa! ɗin kuma?”.
“To tabbas kam wannan matsalar daga nan take boss, Uncle Nasir yasan komai, amma kam bai ƙyautaba, dan nikam ina bala'in ganin girmansa wlhy saboda yanda ya riƙeka, ashe ba har zuciya bane, wannan wane irin zumincine muke fama dashi a wannan zamanin?, kaga yanda aka cukurkuɗe abu saboda kawai buƙatun wasu dason faranta musu, kuma duk idan kaje ka dawo zaka fahimci ita Mami itace akai shirin sakawa a tsaka mai wuya, miyasa sukaso mata wannan mugun ƙullin to?”.
Duk hankalinsu suka maida ga Jawaad da yay shiru yana nazarin kalaman Jabeer na ƙarshe akan uncle Nasir da maganar ƙullin da akaso yima Bilkisu. Cikin son maidosa hankalinsa Hafiz ya zunguresa, kallonsa yay. Hafiz yace, “Mi muke ciki yanzun? Dan ko game da Mami muna buƙatar bincike mugano gaskiyar maganar Jabeer, mizaisa suyi shirin cutar da ita?”.
Guntun Murmushi kawai Jawaad yay ya koma cikin kujera ya zana, kwantar da bayansa a kujeran yana mai lumshe idanunsa, a hankali ya furta, “Wannan shine dalilin zamanmu anan, dan inaji a raina wannan ƙiyayyar da sukaso nuna mata tawuce naƙin son aurenta da Qaseem kawai, akwai wani abu da bamu saniba, dan haka inason sanin anahinma alaƙarta da mutanen gidan”.
Jabeer ya ajiye cokali yana faɗin, “Kamar ta taɓa gayamin Dad yayan mahaifiyartane ubansu ɗaya, kaga kuwa bazai wuce Momy ta ƙitaba akan ƴan ubancin dake tsakanin Dad da mamata, sai dai kuma zata iya yiwuwa ɗin akwai wani abu a ƙasa damu bamu saniba harsai mun bincika tukunna”.
“Kai lamarinfa akwai ɗaurekai, sannan akwai lauje cikin naɗi, aganina tunda basa sonta da ɗansu su rabasu kawai basai sun zalinceta sun haɗata aure da wanda bata saniba”. Hafiz yay maganar cikin takaici.
Aliyu yace, “Kai dai bar son zuciya Hafiz, amma harma nawa Mami take da za'a mata irin wannan muguntar? Yanzu dai boss mikace kai akan batun? Tunda dai ALLAH yasa ta fita daga tarkonsu, yanzu aikin farko dake gabanmu shine Qaseem da Shahudah, baƙaramin yaƙi zasuyi a kankaba da Mami tunda. Shin Ka sanar musu kaine ka canja sunayen ne?”.
Jawaad da duk yake saurarensu cike da nazari yace, “Eh na sanarma Alhaji baba ɗazun, na nuna masa nine na canja, nakuma saka masa zancen Azeema ciki, na tabbatar zuwa safiya zai nema su Uncles da maganar, mukuma sai muyi amfani da wannan damar”.
“Amma Boss baka ganin ka ɗaure kanka da yawa? Taya za'ai ka amshi laifin kai tsaye bayan bamusan mike a ransuba game da batun?”. .
Muryarsa cike da damuwa yace, “Jabeer hakan shine kawai hanya mai sauƙi da zamu bama koma waye ƙafa, sannan Bazaka ganeba, rikicin tsohon nan ya wuce dukkan tunaninka, gara nafito na faɗa masa gaskiyar maganar, harfa ya kafamin sharaɗin saina saki Miemaa, yanzu dai nagama da matsalarsa”.
Dariya sukayi a tare, cike da tsokana Jabeer yace, “To tsakani da ALLAH gaskiya Alhaji baba ya faɗa, ka bama Qaseem matarsa”. Banza yayma Jabeer ɗin, ya miƙe yana kallon agogon hanunsa, “Kunga ɗaya harta wuce, mu tsaida maganar iya haka, zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu nasan Alhaji baba zaisa ai zama akan batun, anan zan fahimci yaren kowa, daga nan saimu ɗora da abinda ya dace kawai”.
Duk sunyi na'am da jawabinsa, kowa ya miƙe yana tattare kayansa kafin su fito, Jawaad tare suka tafi da Hafiz zai ajiyeshi gidan Alhaji baba saboda hanyarsa ce shi, su kuma su Aliyu kowa ya shiga motarsa.

ESTÁS LEYENDO
ƘWAI cikin ƘAYA!!
AcciónTurƙashi, wannanfa shine cakwakiyoyi ba cakwakiya ba, bamma san yanda zan musalta muku kitimurmurar dake cikin book ɗinnan ba sam, dan wani irin ruɗaɗɗen labarine mai cike da abubuwan mamaki da tarin al'ajabi harma da ban haushi, labarin ya taɓo wa...