Shafi na ashirin da biyu
Kuyi manage da wannan babu editing banajin daɗine😥
...............Tun shigowar Qaseem hukumar tasune ya tabbatar akwai abinda ya faru, dama kuma ya samu kirane daga sama akan yazo da gaggawa.
Shigarsa wajen da manyansu suke tare dasu Jawaad ya saka zuciyarsa tsitstsinkewa, musamman tozali da ƴan tawagar Jawaad da yay su Hafeez.
Shi Jawaad ma yana zaune ne kansa a ƙasa saboda ciwon da yake masa, baima san da shigowar Qaseem ɗinba.
Bayan shigowar Qaseem an jira mutane biyu da ake jira suma sun shigo, kafin a fara gudanar da yabo da jinjina akan namijin ƙoƙarin da su Jawaad sukai.
An kuma tabbatar da wanke su Aliyu daga laifin da ake zarginsu dashi wanda yay sanadin zamansu cikin jail.
Take wajen ya ɗauki tafi.
Abinfa zai baka mamaki ko motsi Jay baiyiba a wajen, duk da laifin abokansa da aka wankesu baisashi ya ɗago yama kalli kowa ba sam.
Qaseem ya buƙaci yin magana, dan haka aka bashi damar yi.
Duk da son danne fushinsa da yaketa ƙoƙarin yi hakan ya gagara, sai da muryarsa ta fallasashi, a kausashe yake magana akan yanda aka maida aikin ta bayan fage bayan kuma shi aka damƙawa, ya cigaba da maganganun da suke nuna sukar Jawaad kai tsaye tareda muƙarrabansa, harma yana nuna akwai shiri a cikin lamarin, sai dai idan Jawaad ɗin dama yasan inda Alhaji Kokino yake.
Jay da duk yake sauraren komai yaɗan taɓe bakinsa ba tare daya ɗago ba, ɗakin taron kuma yay tsit an rasa mai bama Qaseem amsar tambayoyinsa, kowa ya zubama Jawaad ido ana buƙatar ƙarin bayani daga garesa, amma abin mamaki tamkarma baisan sunaiba.
Hakanne ya saka Aliyu dake kusa dashi taɓashi kaɗan.
Jawaad ya ɗan ɗago ya kalli Aliyun idanunsa sunyi jajur na gajiya da barci,
“Boss kanafa jin mi yake faɗa”.
Guntun murmushi Jay yayi kawai ya maida kansa yanda yake yana lumshe idanu, sai da Qaseem ya gama ɓaɓatunsa har sir Ahmad ya dakatar dashi sannan ya dawo ya zauna yana huci, ba ƙaramin haushin ƙin kulashi da Jawaad yayba yaji.
Sir Ahmad ne yay bayanin da kowa ya gamsu a wajen bisa shakkun da Qaseem yaso jefa musu akan Jay, daga nan sukai abinda ya tarasu aka sallami kowa.
Dan Jawaad yaƙi cewa kowa komai, koda aka buƙaci jin ta bakinsa Jabeer yaba damar yin bayani, acewarsa shi kansa na ciwo, da yake kowa yasan yanada lalurar ciwon kai da sam idan ya motsa masa bayason takura sai akai masa uziri.
Wannan abunne ya sake fusata Qaseem matuƙa, koda suka fito sai ya tare Jawaad ɗin bisa hanya.
Ko kallonsa Jay bai yiba ya raɓa ta gefensa zai wuce, nanma Qaseem ya sake taresa.
A fusace Jawaad ya fisgo bindigar dake jikin Rose ya nuna Qaseem da ita, dan zuciyarsa a maƙoshi take, shiyyasa sam yaƙi kula Qaseem ɗin tun farko.
Babu wanda yay zaton da gaske Jawaad yake saida ya saki harsashin ciki gadan-gadan akan Qaseem, Aliyu ne ya hankaɗa Qaseem ɗin gefe harbin da Jawaad yayi ya sami ƙofar wani Office dake a wajen.
Nan take wajen ya hargitse da ihu, inda shima Qaseem ya fiddo bindiga wai zai harbi Jawaad, da ƙyar aka rirriƙesa.
Cikin huci Jawaad ya nuna Qaseem ɗin yana faɗin, “Wlhy idan baka fita hanyata ba duk abinda nai maka kaine ka jasa, ka kama kanka Qaseem, karkai wasa da ɗaga maka ƙafan da nakeyi.....?”
Jan Hannun Jawaad da sir Ahmad yayine ya sakashi yin shiru, sai da ya kaisa har Office ɗinsa sannan ya sakesa.
Faɗa ya shiga masa akan waya kaisa aikata wannan gangancin? Yafa tuna Qaseem a samansa yake, baya tsoron abinda zai iya biyo baya?, duk da kowa yasan Qaseem yana shiga rayuwarsa hakan bazai hana a juya abun ta wani ɓangarenba, musamman da akasan Jawaad ɗin yana aiki tuƙuru, wanda hakan yana ɓatama wasu a cikinsu rai da ruguzasu ta hanyoyi da dama sosai.
Ganin Jawaad ɗin baice komaiba shima sir Ahmad ɗin sai yay shiru, dan yasan Jay yanada haƙuri, amma tabbas yanada zuciyar jaraba idan ka kaisa maƙura.
Ruwa ya fiddo a firij ya miƙa masa, babu musu Jawaad ya amsa ya hau sha, sai da yasha fin rabi sannan ya ajiye yana sauke numfashi a gwame.
Ya tsani takura a rayuwarsa, shiyyasa shima bai san takurama kowa, amma Qaseem yaƙi ya riƙe girmansa, ya rasa miya tare masa a wannan duniyar?, tun suna ƙanana Qaseem bayason yaga cigabansa ko farin cikinsa, baisan miyasa hakanba?.
Nannauyan numfashi ya kuma saukewa yana maijin kewar mahaifiyarsa, sosai yake bukatar ɗumi irin na uwa a kusa dashi, sai dai shi tashi ta masa nisan kiwo.........
Sir Ahmad ya katse masa tunani ya dafashi a kafaɗa, ɗago jajayen idanunsa yay yana kallonsa, cikin sigar lallashi sir Ahmad ɗin yake ma Jawaad nasiha akan yacigaba da haƙuri da lamarin mutane, haka rayuwa take, kai kana harkokinka baka damu da kowa ba amma wani shi idanunsa na bisa kanka gaba ɗaya, kowa a rayuwa da kagani akwai tasa gaddarar, maƙiya kuma sune gishirin zaman duniya.
Jawaad ya gamsu da jawaban ogan nasa, dan haka yay masa godiya sosai.
A waje kam sosai hayaniya ta ɓarke, su dai sauran waɗanda ke wajen sun zama ƴan kallo, dan kuwa dai faɗan na manyane.
Inda su kuma manyan hankalinsu ya tashi, da ƙyar aka saka Qaseem a mota aka bar wajen dashi, amma sai iƙirarin kashe Jawaad yakeyi.
Wannan shine dalilin shigowarsa gida yana banbamin masifa🤦🏻♀.

KAMU SEDANG MEMBACA
ƘWAI cikin ƘAYA!!
AksiTurƙashi, wannanfa shine cakwakiyoyi ba cakwakiya ba, bamma san yanda zan musalta muku kitimurmurar dake cikin book ɗinnan ba sam, dan wani irin ruɗaɗɗen labarine mai cike da abubuwan mamaki da tarin al'ajabi harma da ban haushi, labarin ya taɓo wa...