12

14K 1K 81
                                        

ƘWAI cikin ƘAYA!!

Bilyn Abdull ce👌🏼

Shafi na goma sha biyu

............Tun a farkawar da nai a wannan barcin safe da yay nasarar saceni na fahimci lallai ƙaddarar rayuwa ta sake jefoni wani rukunin ajin karatun, dan kuwa babu tantama gidan nan na karuwaine. Wasu hawaye masu ɗumi suka gangaro saman kumatuna, ban damu da sharewa ba na barsu suna cigaba da kwarara tamkar an buɗe fanfo.....
           “Baƙuwarmu kina ganin kuwa kukan nan bai isa hakaba?”.
     Ɗaya daga cikin waɗanda suka taimakeni ta faɗa tana janye hannun da nai tagumi dashi.
     Idanu na ɗago na kalleta, ƙyaƙyƙyawace, sannan yarinya shakaf da shekarunta bazasu gaza kamar nawa ba, banbancina da ita kawai jikinta a murje yake alamar akwai jin daɗi tattare da ita, na sauke ajiyar zuciya ina kauda idanuna daga gareta ba tare da na ce uffanba.
      Ɗayar data shigoce ta katsemu da faɗin, “Sweet gafa Laran gabas can nayi dake akan wasan jiya”.
       Ƴar daɓas ta kwashe da dariya tana zama a bakin katifar, “Bar shegiya kinji Sweet, itadai ai bariki iyawace, kowa kaga yazama wane ya iya allonsa ne, idan ta isa itama ta iya wanke nata”.
      “Kamar kuwa kin shiga zuciyata Sweet, dan nima haka nace mata”.
        Kusan a tare suka taɓe baki, Nazy ta juyo indomie daga cikin tukunya tana ajiyewa gabana, “Sorry bakuwarmu mun barki da yunwa, kinga abincinki nan tun ɗazun tsumayen tashinki mukeyi, kinfa sha barci, saikace wadda bata samun isashen barci daga inda ta fito?”.
      Murmushin yake kawai na mata, sai dai ban iya cemata komaiba itama.
       Ƴar daɓas tace, “Nikam badan jiya kinyi magana ba da nace kodai ke kurmace, ki daure ki amsa mana tambayoyinmu kafin Uwargida ta shigo gidan nan, dan in bata fara samun wani bayani daga garemu ba zamu fuskanci matsalane akan kawoki, kodai kema rayuwace ta nuna miki hanyar zaɓar ƴancin kankine?”.
       “Neman ƴancin kai kuma?”.
      Cikin tsagwaron mamakin daya mamaye fuskata nake jefa musu tambayar tawa.
       A tare suka ɗagamin kai, Nazy ta washe haƙora tana cewa, “Ai duk macen da kika gani a gidan nan tazone domin samun ƴancin kanta, sai dai kisamu banbancin dalilan da suka nuna mana hanyar hakance nasararmu”.
        “Wata sabuwa kenan”. na faɗa a fili batare dana saniba.
       Atare suka maimaita abinda na faɗa ɗin, suka ɗora da faɗin, “Miyasa kikace haka? Kina ganin hanyar da muke bata dace da tsarinkiba kika fito da ga gidanku?”.
       Murmushi nayi ina lumshe ido, wasu hawaye suka sake ziraromin, hannu na saka na sharesu a karo na farko, na kallesu sosai cikin matuƙar tausayawa kanmu, “Ni ba wannan harkar nazo yiba, ƙaddarar rayuwace kawai ta kawoni cikin taku ƙaddarar”.
     Shiru duk sukayi suna kallona, nima ban sake cewa komaiba na zame na kwanta ina cigaba da kukana, tsawon loakaci muna a haka babu wanda ya sake cewa komai, sai zuwa can ƴar daɓas tace, “To ki daure ki tashi kici abincin, sannan idan bamu shiga rayuwarkiba dan ALLAH ki bamu labarinki”.
       Shiru ban motsaba, bankuma iya cewa da ita komaiba, babu abinda ke sukar zuciyata sai halin dana bar ƴar uwata Firdausi a ciki tare dasu Inna, saiko kisan Jazuga danai da hannuna, na ɗago hannuna ina kallo, wasu sabbin hawayen suka sake ziraromin, jinake inama ni Jazuga ya kashe, dana huta, koba komai zan kusantu da iyayena, na rushe da kuka mai sauti ba tare da nasan muryata tayi ƙarfi irin hakanba.
       Akusan tare sukai kaina suna tambayata lafiya?, yanzunma dai basu iya samun amsaba daga gareni har wata mata ta shigo.
     Barina sukai duk suka juya gareta, cikin matukar ladabi da girmamawa suka shiga gaishe ta.
      Amsawa take a dake, yayinda idanunta ke a kaina ko kyaftawa batayi, batare data ce musu komaiba ta nunani da ɗan yatsa.
      Nazy ce tai saurin faɗin, “Uwargida baƙuwace da jiya muka taimaka a ƙofar gidan wasa, Babu ne kuma ya bamu ƙwarin gwiwar hakan, yakuma sanar mana zai faɗa miki da safe”.
         Shiru bata amsa ma Nazy ba, sai takowa da tayi zuwa gabana, da hannunta taimin alamun na miƙe zaune, babu musu na tashi danni tsoro ma ta bani, gata garjejiya da tsaho da ƙiba, kaina a ƙasa murya na rawa nace, “Ina kwana?”.
     Karon farko naji muryarta ta amsa mini, sai dai kallon ƙurullar da takemin ne ya sakani jin na takura.
        “Ya sunanki? Mikuma ya kawoki nan?”.
     Shiru kamar bazance komaiba, wani wanda bansan dashiba ya daka min tsawa, hannu ta ɗaga masa alamar ya bari, niko da naketa rawar jiki sai ta tsugunna gabana tana cemin, “Kinga nutsu faɗamin”.
        Tamkar zan haɗiyi zuciyata na mutu dan tsoro nace, “Sunana Bilkisu, ƙaddarar rayuwace kuma ta kawoni nan ɗin”.
         Batace komaiba ta cigaba da kallona tsawon sakwanni, sai kuma ta miƙe tana faɗin,  “Ƴar daɓas ku bata dukkan kulawa, tana bukatar hutu koda na kwana uku ne, amma zuwa dare kuzo da ita gidan wasa”.
     Da to suka amsa mata cike da ladabi, itako ta fice tana ƙara jin kanta sama.

ƘWAI cikin ƘAYA!!Onde histórias criam vida. Descubra agora