7

12.1K 1.3K 429
                                        

          Barka da juma'a.

  Page 7

.................Mintuna kaɗan budurwar ta dawo da tire babba a hannu, wanda aka jero abubuwan da muka buƙata a kansa.
            Tana ƙoƙarin ajiyewane Jay ya miƙa hannu zai ɗauki ruwan da aka fara kawo masu, a salon da babu wanda ya isa fahimtasa har bily bata kulaba ya tanƙwaɓi tiren ya suɓuce, jikake “Tarats!!! Tass! Tatass!!” kwanikan da suka zube na fashewa, abinda ke cikinsu gaba ɗaya sun koma jikinsu sun wankesu, duk jikinsu ya ɓaci daga shi har bily da bata san mafari ba, a take duk hankalin mutanen dake kusa dasu ya dawo kansu.
              Na ɓata fuska saboda harga ALLAH banji daɗin yanda jikina ya ɓaciba. Cikin langwaɓe kai na kallesa kamar zanyi kuka.
        Da ƙyar Jay yay ƙoƙarin haɗiye dariyar dake neman kufce masa saboda yanda Bily tayi fuska kamar zata fasa ihu, ga mai da yay tsalle harkan fuskarta sai naso yake.
      A fusace  na miƙe saboda ganinma dariya yake neman yimin, dan da gaske haushi naji har raina, maimakon ya mata faɗa amma kuma tsabar wulaƙanci yake neman yimin dariya a cikin mutane, bamma san sanda na fara zazzaga mata masifa akan tayi hakanne da gangan ba, yanda ta rikice ba ƙaramin tausayi ta baniba, amma kuma uwar mi take kallo da zata wankemu haka?, shima jinake kamar na juya na talle masa ƙeya yasin.
           Jawaad ya tsaya kawai yana kallon bakin Bily dake masifa, babu shiri murmushi ya suɓuce masa, ganin tamkar abin nata da gaskene shima sai ya miƙe, cikin son maidota hayyacinta ya nema riƙo hannunta, amma sam taƙi yarda, dan danan wasu ma'aikatan nasu sukazo, da alama suɗin manyane, haƙuri suketa bamu amma naƙi saurarensu, daga ƙarshema nai ficewata, shikuma yay azamar biyoni yana faɗin, “princess! Princess! Please ki tsaya mana”.
     Ƙo juyowama banyiba na nufi motarmu na buɗe zan shige, saurin riƙe murfin yayi yasha gabana alamar hanani shiga motar, ya wani marairaice yana lallashina, wlhy da kunsan yanda zuciyata ke harbawa sanda muke a wannan yanayin da kun bala'in tausayamin, a haka budurwar da wasu ma'aikatan wajen suka iso suka taddamu, haƙurin suka cigaba da bamu, sai da muka ɗan garasu da kalamun cewar bazamu sake zuwa wajenba tunda basusan kimar Customers ba kafin na nuna na haƙura da ƙyar, dan zuwa yanzu na dawo hankalina akan shirinmu.
     Sun buƙaci mu koma wajen a bamu wani abincin amma na tubure akan bazan koma ba, sai dai a haɗo mana takeaway, ba musu suka amince da bukatata, ganin sunbar wajen ne ya sani sauke ajiyar zuciya ina matsawa baya saboda kusancin da muka samu ni da shi neman karya ƙwarin gwiwa da nake bama kaina ya keyi, gashi yay masifar tsareni da idanunsa.
     Shima matsawa yayi, ya nuna min mota alamar na shiga yana zubamin harara, “saurin shigewar nayi kuwa, ya rufemin murfin ya zagaya ɗayan ɓangaren, da sauri gimba dake bayanmu tsaye yana kallon dramar tamu ya buɗe masa, hanasa rufewa yayi, saima ya zauna ƙafafunsa duka a waje. A haka budurwar ta dawo ɗauke da takeaway ɗin da muka buƙata, gimba ya amsa ledojin, shi kuma ya miƙa mata atm card ɗinsa tare da wata takarda yana magana ƙasa-ƙasa, “Saboda baƙwason ya tona muku asiri kuka kasheshi?”.
     A firgice budurwar ta kalli Jay, sai kuma ta hau waige-waige jikinta sai tsuma yakeyi.
    Ya sake faɗin, “Ki daina ɓatama kanki lokaci, akwai address ɗin inda zaki sameta (ya nuna bily) a jikin takardar nan ranar lahadi, yarage naki kizo ko kiƙi zuwa, sauran bayani mahaifinki zanyimawa”.
     Sake rikicewa tayi, jikinta sai wata masifar tsuma yakeyi. Yanda taketa kallonsa a firgicene ya sakani tabbatar da maganar bamai daɗi ya faɗa mataba, tabar wajen da sassarfa, yayinda gimba ya take mata baya domin amso atm ɗin idan sun cire kuɗinsu.
       Wato dai duk yanda nake tunanin aikin nan namu yafi ƙarfin tunanina, irin wannan makirci haka tamkar wani shirin film.
 
          Gimba bai wani jimaba ya fito da ɗan hanzarinsa, motar shiru tamkar babu mutum mai numfashi, nidai takurace ta hanani yin ƙwaƙwƙwaran motsi, danma ALLAH ya soni yanzu a gaba nake ba kamar yanda muka zoba, shiko bansan mi yakeyiba, dan nakasa kallonsa koda ta mirror ne, abinda ya faru a wajen da wanda nayi keta dawomin a rai, sai naga kamar na zaƙe da yawa, ko a gidan uwarwama na samo ƙwarin gwiwar zuba masifar irin haka?’.
       Sai da gimba ya tada mota sannan yace, “Boss zamu koma station ne?”.
    Shiru bai bashi amsaba har muka fice daga gate ɗin wajen muka hau titi, ni nama ɗauka ko barci yakeyi, sai jinai ya bashi amsa da,
      “A.Y....”
Ban fahimci ma'anar maganarba, amma shi gimban naga kamar ya gane mi yace. Wayata daketa vibration tun ɗazun na kalla, yah Qaseem ne yanzuma, wannan shine kira na kusan bakwai kenan, tun muna cikin wajen cin abinci kiransa keta shigowa, sai dai bansan miyasa nakasa ɗagawa ba, a hankali na sauke ajiyar zuciya jin wayar ta yanke, kasheta nai baki ɗaya ma, dan bansan dalilin kiranba, idan kuma na ɗaga bansan mizance masaba, bankuma saniba ko ɗagawar zai iya zama laifi a wajen wanda muke tare. Isowarmu wani gida mai ƙyau da tsarine ya yanke tunanina, tunda aka buɗe mana gate muka shigo naketa bama idona abinci nidai, gimba ya tsaida mota ya buɗe ya fita, ni dai banyi yunƙurin fitarba harshi aka buɗe masa ya fice, akan idona yabar wajen ya nufi wata ƙofa mai alamar shiga ainahin cikin gidan, na sauke ajiyar zuciya kaɗan ina lumshe ido, fatana yazam shikenan yace a maidani station.........
       Kallon gimba dake bani umarnin shiga nai da sauri, yay murmushi yana sake maimaitamin, “Ki shiga inji boss”.
      Jinai tamkar na fasa ihu, amma bani da ikon cewa ba hakaba, dole na fito ina sake bin harabar gidan da kallo, gimba ne yaymin jagora har ciki, ‘Masha ALLAH’ na faɗa akan laɓɓana saboda haɗuwar da falon yayi, babu kowa a ciki sai ƙamshi mai daɗi dake tashi a cikinsa....
     Gimba yace, “Ki shiga nan saiki gyara jikinki”.
    Murmushi naɗan masa ina jinjina kaina, na nufi ƙofar raina cike da tsoro da mamaki, sai faman tambayar kaina nake ko ina matar gidan? Dan naji gidan tsit. ‘Kika sani ko tare suka shige ciki?’ zuciyata ta ayyana min haka, bakina naɗan taɓe, na tura ƙofar na shiga da sallama. Ɗakine babba, akwai komai na amfani kuma a ciki, sai dana gama ƙare masa kallo kafin na nufi ƙofar da nake ƙyautata zaton bayine, bayan na rufe ƙofar sai kuma nai tsaye ina ƙarema kaina kallo ta cikin madubin dake toilet ɗin, Toni ta inama zan farane? Ni bawasu kayane dani ba, gashi kayana sun ɓaci sosai, na zare rigar saman da ya bani, wadda kasancewarta fara ta ɓaci sosai, hakama wandona, amma da yake baƙine shi ba gani akeba, sai ƙamshin miya da yake da mai dakemin naso a jikine zaisa ka gane ya ɓaci shima sosai, shawarar cirewa na wanke nayi, dan haka na cireshi a ɗarare.
       Ban fahimci kuskurena na jiƙa wandonba sai dana gama wankesa nanfa tunanin inda zanje na shanya, da kuma ta yanda zanma fita shanyawar tunda bawasu kayanne daniba yazomin. jinai hawaye sun cika idona, ‘Ni balki naga takaina’ na faɗa a hankali ina haɗiye kukan dake neman zuwamin. A bayin na shanya wandon na fito ɗaure da sabon tawul dana gani, na zauna a bakin gadon na rabga tagumi ina addu'ar neman mafita.
     Nai firgigit jin an turo ƙofar kamar a fusace, fuskarta a haɗe ta shigo hannunta ɗauke da leda yellow mai tambarin M&N, cike da kallon tsana ta miƙamin ledar, amsa nai nidai cikin girmamawa amma ina mamakin yanda takemin a ƙasan raina. Juyawa tai zata fice na bita da kallo, sai da ta buɗe ƙofar sannan tace, “Ana jiranki” kawai ta fice abinta.
     Numfashi na sauke a hankali, na buɗe ledar na fidda kayan ciki, wandone da riga duk baƙaƙe, sai baby hijjab fari irin waɗanda nake sakawa, tashi nai na saka kayan, sunmin bala'in ƙyau, sai dai inajin kunyar fita a haka sosai, dan sun wani lafe a jikina dukda dai rigar bata matseniba, bani da zaɓin daya wuce daurewa na fita a hakan kawai, danma baby hijjab ɗin ya rufemin ƙirji, na maida kayan dana cire a jikina cikin ledar harda wandon dana jiƙa ɗin, kaina a ƙasa na fito daga ɗakin, zuciiyata sai harbawa take da sauri-sauri.
           Wani iri naji a raina ganin kusan su biyar ne a falon, sai na kumajina a matuƙar takure musamman saboda kayan dake jikina, ƙarasawa nai cike da aro jarumtar dole ganin su hankalinsuma ba'a kaina yakeba, sallama nai duk suka amsa mani, na gaishesu da girmamawa nanma suka amsa, na kula kamar kallon mamaki sukemin irin kamar basuyi tunanina ganina a wajenba, hakan sai ya sakani jin wani iri, na saci kallon dodon nawa, dan tunda na fito baiko ɗaga kai ya kalli sashen da nakeba, yana zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya tamkar wani basarake, idonsa na bisa takardun dake hannunsa, shima ya canja kayansa zuwa farin wando da baƙar t-shirt mai gajeren hannu, rigar ta kwanta masa a jiki, hakan yasa ta fidda ainahinsa na ƙaƙƙarfan mutum.......
       “Bismillah zauna mana”
Oga Hafiz ya katse min satar kallon boss dana shagala yi, kaina na jinjina na zauna a inda ya nunamin ɗin a ɗarare.

      Tun fitowar Bilkisu a idanun Jawaad ne, duk kuma abinda take yana kallonta ta gefen ido, amma babu wanda zai iya fahinta, idan akai dubi da yanda ya maida dukkan hankalinsa ga takardar hannunsa, ɗago idanunsa yay yana kallon Aliyu dake danna lap-top, yace, “Aliy ya buɗe ne?”.
      Girgiza kai Aliyun yayi yana guntun tsaki, ya juya masa fuskar lap-top ɗin da faɗin, “Ni banama zaton yana amfani da accaunt ɗinnan gaskiya, boss wai mizai hana mu aika wani cikinsu kawai, sai naga haka kamar zaifi komai sauƙi da muzauna a bayan fage muna wahal da kanmu, tunda bamu da tabbacin yarinyar zata bamu haɗun kai”.
    Kafin Jawaad ya bashi amsa Rose dake gefensa tanata wani cika da batsewa tai caraf ta amshe zancen, “Boss dabaran Aliyu yayi sosai, kaga sai a aika yarinyarnan kawai cikinsun”.
       Wani mugun kallo da ya bama kowa mamaki a wajen Jawaad ya watsama Rose, sai kuma ya ɗauke kai batare da yace mata komaiba.
         Duk zuba masa ido sukai suji ko zai bama rose amsar maganarta, ni dai kaina a ƙasa ban ɗagoba inata wasa da yatsun hannuna, na ɗan saci kallon nasa nima sai naga ya cigaba da duba takardar hannun nasa ma tamkar baisan mi akeba. Tsawon mintuna bakwai muna a haka kafin muga ya ajiye takardan hannun nasa ya miƙe, wata ƙofa ya nufa, duk suka sake binsa da kallo harni da nakeyi a munafunce. yana shigewa duk suka maido dubansu gareni, inaga ganin yanda na takura kaina ne da ganin kamar bare a cikinsune ya saka oga Jabeer sakarmin murmushi, cikin tsokana yace, “Anya kuwa wannan ƙanwar tamu ba matsoraciya bace?”.
      Karon farko da nai murmushi, na ɗan kallesa na ɗauke idanuna da faɗin, “A'a Sir”.
    Dariya duk sukayi, amma banda Rose da ta ɗauke kai tana taɓe baki.
      Oga Aliyu dake danna lap-top har yanzu yace, “To idan ba matsoraciya bace ki saki jikinki damu, munan duk yayunkine ba surukaiba, minene sunanki?”.
      Naɗan kalli sashen da yake fuskata ɗauke da murmushi nace, “Bilkisu Adam makah..o”.
        Na ƙare maganar a hankali saboda yay dai-dai da fitowarsa daga ɗakin daya shiga, ya ɗoro baƙan jacket saman kayansa, ido muka haɗa, nai saurin janyewa nawa ina haɗiye murmushin kan fuskata saboda maganar da su Hafiz sukeyi na cewar “Ashe mai babban sunace, duk mai wannan sunan kuwa jarumace”.
     Duk dariya sukayi, amma banda rose da shi da muka sake haɗa ido a bazata, saurin janye idanuna nayi zuciyata na wata irin harbawa, hanyar ƙofa ya nufa yana faɗin, “Kumuje” Yana ƙoƙarin gyara baƙar jacket ɗin daya ɗoro saman rigarsa.
     Rose ce farkon miƙewa ta fice, niko ban motsaba sai da suka gama fita sannan na zama ƙarshe.
          Jikin motar da mukazo na hango rose tsaye, ta wani haɗe fuska, shi kuma yana daga gefe waya a kunnensa, hannunsa ɗaya a aljihun farin wandonsa, ido muka haɗa nai saurin janye nawa nidai, dan sam banyi zaton sashen da nake yake kalloba ma, a raina ina mamakin yanda duk sanda zan saci kallonsa nakan kama idanunsa a kaina shima, sai naji haushi na balla masa harara ta gefen ido duk da baisan inaiba.
     Duk tsaye mukai muna jiran ya kammala, kusan mintuna uku kafin ya sauke wayar ya tako wajen motar da rose ke tsaye, muma duk muna kusa, ya kalli Hafiz yana faɗin, “Yanzu yaya za'ai kenan?”.
         Hafiz yace, “Boss inaga ku koma Office, ni da rose da Aliyu zamuje can anguwar mu sake bincikawa, maybe mu samu wani a gidan yanzun”.
     “Okey hakan yayi” yay maganar yana yunƙurin buɗe motar, dole Rose data cika fam da haushi ta matsa, har zai shiga ta katse hanzarinsa da faɗin, “Boss nikam da sun wuce, sai na biku, zan ɗauka wayata dana manta a office, zan bisu a baya tunda nasan anguwar”.
       Ɗagowa yay yana kallonta fuskarsa babu walwala, ya janye idanunsa a kanta batare da ya bata amsaba ya maido kaina dan duk kallonsu mukeyi, “Mimaa! Shiga mota muje, ke kuma ki bisu kubiya ta station ɗin tare sai ku ɗauka wayan ku wuce”.
     Duk da naga idanunsa a kaina suke sai ban fahimci dani yakeba saboda sunan daya ambata, gashi har yayi shigewarsa motar.
      Jabeer dake kusa dani yay murmushi, “Dake yake fa, kije kutafi”.
    Kaina na jinjina masa kawai ina murmushin ƙarfin hali da sake juya sunan a raina, ‘Mimaa;? To wannan sunan kuma daga ina haka?’. Na ƙarasa zan shiga gaba, sai dai rose taƙi matsawa a wajen, na kalleta nace, “Zan shiga ciki maa”.
    Shiru bata motsaba, bakuma ta tanka minba..............✍

Rose yau kinga idi wajen bily team, dama hauhinmu sukeji😥🤐.

Asha weekend lafiya😜😑😉🤗🤗.



ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻

ƘWAI cikin ƘAYA!!Onde histórias criam vida. Descubra agora