Page 55
.................“Baba bazan iya barin anguwarnan ba sai da ita”. “Bazai yuwuba Jawaad, kaje itama insha ALLAH lafiya zata fito, dana koma yanzu zan fiddotane itama”. “Baba kaima fa bazai yuwu ka zaunaba, dan zamanka akwai haɗari Sadiq zaizo ya ɗaukeku tare, kaje ka haɗa duk wani abunka mai muhimmanci”. “To shikenan ɗana, ALLAH yay maka albarka sai ya zo”.
CIKIN JIRGI
Tun ɗaga gadon farko da Bilkisu tayi jikin Alhaji kokino ya bashi, to amma yasan akwai mai tsaron wajen koma waye tsautsayi ya kaisa sai dai gawarsa. Sai dai kuma ƙarfin gwiwarsa ta sare lokacin da yaga zoben dake a hannunsa yana canja kala zuwa baƙi, gabansa yay matuƙar faɗuwa, gashi babu damar kiran waya, a take komai nasa ya fara kwancewa lokacin da zobe tsafinsu ya shiga hasko masa abinda bilkisu keyi, sai dai ALLAH ya hanashi ganin fuskarta sam sai duhun inuwarta kawai yake gani harta ɗauki tukunyar data ɗauki tsawon shekaru a jiye babu wani mahaluki da ko yatsansa ya taɓa taɓata, sai maman yara da idanunta suka gani itama kuma saida ya sakata tai nadamar hakan, tanama can cikin nadamar ma (Masu karatu Alhaji kokino fa baisan yanzu maman yara bata wajen yaransa ba, dan randa ƴarsa ta saka masa maganin barci koda ya farka a washe gari har an maida masa wayoyinsa, babu wata kuma alama da Jawaad ya bari dazai iya zarga, shikuma da yasan babu wani mahaluki da zai iya masa makamancin haka sai bai kawo komai a ransaba, a washe garin ya bar ƙasar batare da yayi waya da yaransa akan komaiba. ALLAH kuma ya hana shaiɗanun dake taimaka musu fahimtar komai balle shugaban nasu na dodon tsafi damar sanar masa.
Gaba ɗaya ya jiƙe da uwar zufa sharkaf kamar ana masa wanka da ruwan zafi, jiyake tamkar ya rikito jirgin ƙasa dan tsabagen tashin hankalin da yake a ciki, gashi sauransu kusan awa ɗaya da rabi kafin ma su sauka. Lallai wannan ko wanene a cikin gidansa sai ya ƙarar da dukan ahalinsa bama shi kaɗaiba.
Jawaad kam kai tsaye gidan Alhaji babba ya nufa, sun fito masallaci kenan sai ganin Jawaad ɗin yayi ya fito a mota, sai dai yanayinsa yay masifar ɗaga hankalinsa. Tambayoyi ya shiga jera masa, Jay dai bai amsa masa ko gudaba a ciki ba, “Baba wannan ba lokacin amsa tambayoyi bane”. Ya faɗa yana nufar cikin gidan da tukunyar a hannunsa dan da duk a wajen gate suke inda Jawaad ɗin ya faka motarsa. Alhaji babba da ciwon ƙafa ya matsamawa a kwanakin nan ga yawan mafarke-mafarke da faɗuwar gaba da yake yawanyi yabi bayan Jawaad jiki a sanyaye, iskesa yay tsaye tacan bayan ɗakunansu ya ɗaga tukunyar zai fasa bakinsa ɗauke da addu'a. “Kai wai minene kake haka? sai kace wani matsafi?”. Jikake “Tassss!” Jawaad ya buga tukunya da ƙasa.
Fashewarta tayi dai-dai da faruwar abu uku a zahiri, biyu a ɓoye.Na farko shine saukar jirgin da alhaji kokino ke a ciki bisa ƙasa. Na biyu mummunar faɗuwar gaba ga duk masu alaƙa da tukunyar, na uku faɗuwar Umm-Anum dake a kicin tana dafama Abbu shayi da yake a gidanta yake yau. Na baɗinin kuwa daga can fadar shaiɗancinsu ya faru.
Wasu irin mugayen layune manya-manya guda uku a ciki, sai ƙananun allurai da wasu irin abubuwan surkulle da baisan minene ba shima, sai ruwan kuwa da suke ciki na jini ne sai wani uban wari ya keyi maiban tashin hankali, Alhaji Babba ya waro idanu waje jikinsa na rawa da toshe hancinsa da hannu yace, “Muhammad minene wannan? A ina ka samoshi ni Nuhu?”. Taga-taga Jawaad yay zai faɗi idanunsa a matuƙar jazur, Alhaji babba yay saurin riƙosa. Atare suka sauke ajiyar zuciya, da sauri Jawaad ya zare hanunsa daga na Alhaji babba ya nufi cikin gidan, hankalin Alhaji babba sake tashi yayi, ya kalli tukunyar da kayan ciki ya kalli hanyar da Jawaad yabi, ya juya zai bishi sai gashi ya fito ɗauke da ashana da gallon ɗin fetur na Genretor. Akan kayan ya zuba ya ƙyasta musu wuta. A take gidan ya ɗauki wani irin mahaukacin ƙauri mara daɗin shaƙa, sai ƙananun motsi kamar ana guje-guje, suka hau waige-waige suna dafe kunnuwansu da hannu da sauri, sai kuma aka fasa kuka da wata irin murya mara daɗin saurare. Ana ƙwalla kiran sallar isha'i gidan kuma yay tsitt dan masallacin idan aka kira salla kakanji tamkar a cikin gidan akeyi tsabar kusancin da suke dashi. Jagwab Jawaad ya zauna a ɗan dakalin da aka shuka fulawoyin gidan, ya dafe kansa yana karanto hasbinallahu wani'imal wakil. Sai kuma ya miƙe zumbur saboda tunawa da bilkisu da baba, lallai duk inda Alhaji kokino yake yanzu jirginsu ya isa sauka ƙasarnan. “Baba ina zuwa ya faɗa yana nufar gate cikin zafin nama. Sake binsa da kallo Alhaji babba yayi harya fice.
Jay ya buɗe mota zai shiga saiga drivern gidan Ummah babba ya kawo Batool, baiko kallesu ba duk da ɗaga masa hannu da takeyi ya buɗe motarsa ya shiga tare da yin reverse yabar anguwar da mahaukacin gudu kamar zai tashi sama.

KAMU SEDANG MEMBACA
ƘWAI cikin ƘAYA!!
AksiTurƙashi, wannanfa shine cakwakiyoyi ba cakwakiya ba, bamma san yanda zan musalta muku kitimurmurar dake cikin book ɗinnan ba sam, dan wani irin ruɗaɗɗen labarine mai cike da abubuwan mamaki da tarin al'ajabi harma da ban haushi, labarin ya taɓo wa...