Chapter fourty- seven

403 53 6
                                    


This page is for you @NabilaHayatu❤️

Washe gari tun a school Samha take ta murna tana Allah Allah ta dawo gida don sunyi waya da Anty katibe tace jirgin su ya sauka suna gida.

Ba abunda yake sata murna illa ganin Azirak, don tayi missing yaron sosai.

Ko data dawo gida da murna suka rungume juna, taje ta dauki Azirak kamar zata mayar dashi cikinta don tsabar murna.

Shima dariya ya dinga yi dayaga anata faman tsale tsale dashi.

Bayan sun gaisa da Anty katibe, straight dakinta ta wuce dashi.

Shi kam sai faman mata shirme yakeyi irin nasu na yara, itama biye mishi ta dinga yi sunata wasa.

Sai zuwa la'asar tukuna ta sauko dashi don ya samu yaci abinci.

Bayan Anty katibe ta bashi abinci, Samha ta sake dauko shi suka fito cikin gida.
Nan garden sukaje ta zaunar dashi kan carpet grass sunata wasa.

Bayan kusan 30 minutes motar Sabah tayi
horn, d'aya daga cikin security din yazo ya bude mishi gate ya shigo yayi parking ya fito daga cikin motar, tafiya ya soma yi cikin harabar gidan. Dayake baban gida ne. Daga gate zuwa tsakar gidan ma sai kayi d'an tafiya.

Sai dayazo dai dai wurin garden din ya hango Samha tare da Azirak sunata faman wasa hankalinsu kwance, sai faman guje guje sukeyi tana kokarin kamo shi.

nan take yaji zuciyarsa ta narke abun ya burgeshi sosai, zuciyarsa ta soma hasko masa wani yanayi na daban.

Har ya soma ji tamkar Samha ce da babynsu suke guje guje haka.

Duk tsayuwan nan dayayi yana kallonsu Samha bata san ya dawo ba, gabadaya hankalinta na kan Azirak.

Sabah ya zira hannunsa cikin aljihu ya ciro wayarsa, cameransa ya kuna, yayi saitin daidai inda ta dauki Azirak tana mishi cakulkuli yana dariya ya dauke su hoto.

Dubawa yayi yaga ba karamin kyau sukayi ba. Nan da nan yayi saving ya mayar da wayar cikin aljihunsa ya soma karasowa inda suke.

kamshin turaren signature perfume dinsa taji nan take tasan shine yake tafe.

Cikin sauri ta waiga taganshi tsaye a bayansu, kyakyawar fuskarsa dauke da murmushi.

Itama tsayawa tayi tana kallonsa daga bisani tace "Sabah har ka dawo".

Sabah yace "na dawo kanwata".

Azirak ne ya rarafo yazo ya tsaya dab da inda Sabah yake tsaye ya soma kamo kafar wandonsa.

Sabah ya sunkuya ya dauki yaron yana kare masa kallo yace "kanwata ya naga yaron nan yana kama dake sosai haka?"

Samha ta zaro ido tace "da gaske? Haka mutane suketa fada".

Sabah yayi dariya ya matso dab da ita sa'anan yace "kinga nima haka wata rana zaki haifo mun babies masu kyau irin haka".

Kunya ne ya d'an kama Samha ta sunkuyar da kanta kasa.

Sabah yace "Allah da gaske nake ba wasa ba"

Idanunsa ne suka sauka kan dan karamin waist dinta yakai hannu kamar zai shafa tayi sauri ta kauce tana watsa masa harara.

🥀ZABIN SAMHA🌹(YAYA ko MIJI)?Where stories live. Discover now