Chapter Seventy -Seven

735 54 2
                                    

Samha muryanta na rawa tace " nan fa kitchen ne ya kakeso tayi? Knocking zatayi kafun ta shigo ko meye? ".

Tsaki Sabah ya buga cike da jin haushi ya juya ya fice daga cikin kitchen din.

Ajiyar zuciya Samha ta sake nan take ta nema yunwar ta rasa ta ajiye the plate din abincin a gefe ta fito. Ko data fito bata ga kowa a parlourn ba ta soma kwadawa sophie kira, taji shiru ba'a ansa ba. Haurawa sama tayi tunani kala kala na mata yawo aka don tasan yarinyar ba fada zatayi ba. Amma toh da Ammi ce tazo ta tadda su a hakan fa? Ya zasuyi? Nan take ta tsinci kanta cike da tsananin fargaba.

Da dare misalin karfe bakwai da rabi suna zaune kan dining suna cin abincin dare gabada'yansu sun halara. Anty Fanneh da Abbah suketa faman hiransu banda Sabah da Samha da sukayi shiru suna sauransu. Sabah sai faman latse latsen waya yake Samha tanata satan kallonsa ta kasan idanunta. Suna cikin haka taji wayarta tayi vibrating kusa da ita allamun sako ya shigo. Daukowa tayi ta soma dubawa.

Sako ne daga Sabah kamar haka "ki sameni a daki idan mun gama"

Tana gama karantawa ta da'go ta dubeshi, taga still idanunsa na kan waya, ta tura mishi da reply din toh.

Abbah ne ya soma fadawa Anty Fanneh cewa ya kamata babynan aje America a haifesa ya samu full citizenship. Dariya kawai Anty Fanneh tayi tace ita dai abarta anan babu wani kasan wajen da zataje ta haihu. Sosai suka zurfafa Abba nata tsokanarta kamar wasu sabbin aure ko kula dasu sabah basuyi ba. Sabah ne ya fara mikewa yayi musu sai da safe sa'anan ya haura sama zuwa dakinsa.

Sophie tazo ta soma tatara dining, Samha itama ta mike tayi musu sai da safe sa'anan ta haura sama zuwa dakinta. Bayi ta fada taje tayi tayi wanka ta dauro alwala sa'ananta fito tayi Sallan ishah hade da shafi da wutr. Bayan ta idar ta mike ta shafa mai da humran ta mai dadin kamshi sa'anan tasa kayan baccinta ta zira hijab sa'anan ta fito tayi hanyar dakin Sabah.

Yana zaune a gefen gado daga shi sai bakin wando a jikinsa yana aiki akan system, yaji tayi sallama ta shigo. Dagowa yayi ya zube mata manyan idanunsa yana kallonta ya ansa sallamar. Ganin ta tsaya bakin kofa taki karasowa ciki ne yasa ya da'ga mata gira daya hade da fa'din "mallama lafiya kika tsayawa mutane a bakin kofa haka?"

Still bata tanka shi ba tana tsaye tana jinsa. Ajiye system din yayi a gefe a ransa yace "yan rigimar na kusa kenan". Yana tare da Samha tun bai san yanda ake rarashin mace ba har yazo ya koya tsabar iya shagwabanta, akanta ne kadai ya tsinci kanshi da iya tolerating shagwabar mace, shi ada da ko kallo mace bata isheshi ba idan tana abunta amma sai gashi yanzu ya tsinci kanshi da mikewa yasoma takowa har yazo ya tsaya inda take.

"Menene?" Taji ya tambayeta ha'de dasa hannu ya da'ago habarta yana kallon cikin kwayar idanunta.

"Ba komai" ta fada mishi tana kawar da fuskarta gefe.

Hannunta ya riko cikin nasa sa'anan ya karasa bakin gadon da ita ya zaunar da ita kan laps dinshi hade da kwantar da fuskarta bisa kafadarsa har tana iya shakar daddaden kamshin jikinsa. A hankali ya soma tambayarta. "what's wrong baby? Wani abu kikeso ne?"

Girgiza mishi kanta kawai tayi.

"Toh menene?"

A hankali ta soma motsa lips dinta tace "dazun da muka fita dasu Khadie na hadu da Jabbar a mall. Meyasa baka sanar dani cewa zai koma can kasar mahaifiyarku da zama ba".

Ajiyar zuciya taji ya sake, ya lumshe idanunsa a hankali sa'anan ya budesu can taji ya soma fa'din " na hadu dashi last week, naje can gidan doctor Sageer inda yake da zama. Abba yace mun naje na dubashi".

"Toh meyasa baka fada mun ba? Sabah meyasa bakasan discussing anything family related dani, aside from being your wife nima fa yar'uwarka ce yanzu. Bana jin dadin yanda kake boye mun wasu abubuwan. Kuma inaso ka dinga jan yan'uwanka a jiki, zumunci nada matukar muhimanci, ga mahaifiyarka ma ban taba jin ka dauko mun batunta ba. Ban san meyasa ba. Dan Allah ka dinga kokari kana zumunci da ita".

🥀ZABIN SAMHA🌹(YAYA ko MIJI)?Where stories live. Discover now